• This is Slide 1 Title

    This is slide 1 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

  • This is Slide 2 Title

    This is slide 2 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

  • This is Slide 3 Title

    This is slide 3 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

Thursday, February 28, 2019

JARABAWAR RAYUWA,QIYAYYA KO SOYAYYAR ALLAH GA MUMINI?

Allah Ta'ala ya halicci bayinsa,kuma ya fifita wa'yansu bayin akan wa'yansu.Amma ana gane soyayyar Allah akan bawansa tahanyar:
Kyawun halitta?,
Tarin dukiya?,
Sarauta?,
Mulki?
Nasaba?,
Yawan 'ya'ya? .
Koshakka babu Allah yana fifita/son bayine masu jin tsoronsa tahanyar sadarda umurninsa danisantar sa6a masa.
Sannan wani hukunci na Allah yakan jarraba bayinsa domin yatabbatarda masu imanin gaskiya dakuma masu rauni/ko imanin qarya.Kamar yadda yafada acikin littafinsa mai tsarki,suratul Baqarah ayata 213 da ayata 155:
قال الله تعالى:أم حسبتم أن تدخلوا الجنةولمايأتكم مثل الذين جلوامن قبلكم ،مستهم البأساءوالضراء وزلزلواحتى يقول الرسول والذين ءامنوامعه متى نصر الله،الآ إن نصر الله قريب(٢١٤).
Ma'ana :Allah yana fadama manzonsa dasauran muminai ,kuna tsammanin zakushiga aljannah alhalin irin abunda yasami wa'yanda suka gabaceku baizo makuba,tsananin talauci ya shafesu,da rashin lafiya(kamar yadda Dan Mas'ud,Dan Abbas,Mujahid,Sa'eed Dan Zubair dasauran malamai suka fassara ) kuma aka girgizasu girgizawa mai tsanani(ai aka jarrabesu da tsoron makiya/abokan gabansu)saboda  tsananin jarrabawa hartakai manzon Allah dasauran muminai suna tunanin yaushe nasara zata zo masu(bawai suna ganin Allah bazai kawo masu dauki/agaji bane,amma saboda qunci dasuka kasance ciki yasa suke addu'ar samun nasara akusa)sai Allah yace kusaurara!! lallai nasarar Allah akusadaku take(gaf kuke dasamun yayewar musibar dakuke ciki.
ولنبلونكم بشىء من الخوف والجوع ونقص من الأموال والأنفس والممرات وبشر الصابرين.....
Tabbas zamu jarrabeku

dawani abu na tsoro,da yunwa,da tauyewar dukiya da rayuka(mutuwar makusanta,'ya'ya,mata,iyaye,abokai dasauran makusanta),da tauyewar 'ya'yan itace,sai Allah yace acikin wa'yannan musibu idan suka samu bayi ,to kayima masu hakuri bushara.Wanda idan musiba ta samesu saisuce;lallai damansu daga Allah sukafito(shiya haliccesu)kuma tabbas zuwa gareshi zasu koma.
 Akwai ayoyi makamanta wa'yannan dayawa.Sannan Hadithi yatabbata daga Manzon Allah S.A.W:
أشد الناس بلاء الأنبياء ثم الصالحو،ثم الأمثل فالأمثل،يبتلى الجل على حسب دينه،فإنكان فيدينه صلابة زيد قلابة،وإنكان في دينه رقة،جفف عنه،ولا يزال البلاء بالعبد حتى يمشي على الأرض ماله خطيعة
Wanda sukafi samun jarabawa mai girma arayuwa, sune annabawa,sai salihan bayi,sannan hawa -hawa(gwargwadon imanin mutum gwargwadon jarabawarsa arayuwa)Allah yana jaraba bawa gwargwadon addininsa(imaninsa)idan bawa yakasance mai qarfin imanine sai jarabawar taqara qarfafa imaninsa,idan kuma yana da rauni sai jarabawar ta'inganta masa imaninsa,bawa mumini bazai gusheba Allah yana jarabashi har sai yakai yana tafiya asaman qasa bashida zunubi kokadan
قال رسول الله صل الله عليه وسلم:مايزال البلاء بالمؤمن والمؤمنة في نفسه وولده وماله حتى يلقى الله تعالى وما عليه خطيئة.
Hakanan imam Attirmizi Rahimahullah yafitar da hadithi manzon Allah S.A.W yace:Mumini ko mumina bazasu gusheba cikin bala'in rayuwa(jarabawa)acikin jikinsa,da 'ya'yansa da dukiyar(talauci ko asarar dakiya) har mutum yahadu da Allah bashida laifi kokadan.
Dan haku yaku 'yan uwa masu imani,karmudinga jin munfi wa'yansu dan Allah yasa munada wani abu ahannunmu,kamar yadda rayuwar yanzu ta koma idan bakada kudi kai ba kowa bane kuma bakada mutunci.idan kanada wani abu kuma komai lalacewarka to za'a dunga mutuntaka.wadata da talauci duka jarabawane.Kasancewarka cikin:
Walwala,
Wadata,
Matsayi na muqami
Baya nuna cewa kafi wane/suwaneba awajen Allah,ko kadauka kai kafisu kusanci da Allah.A'a ganin damar Allah ne.
Idan har kanacikin Wanda Allah yawadata yi amfani dadamar wadatarka kafin rashin damar,Kataimaki bayin Allah matuqar kasamu iko,Kamar yadda manzon Allah S.A.W yace duk cikin mutane babu wani danafi amfana da dukiyarsa kamar Abubakar R.A. kaga kuwa da imani shiyakesa atara dukiya da kuwa duk duniya cikin halittun Allah baza'a samu wanda yafi manzon Allah S.A.W tarin dukiyaba.
Allah yabamu ikon cin jarabawar dayake yimana,yaqara rufa mana asiri,yagaafarta mana laifukanmu.

Saturday, February 23, 2019

KARMU MANTA DA 'YAN UWANMU DAKE YANKIN BATSARI,JIBIYA,SAFANA DA ZAMFARA

AL'UMMA MUCIGABA DASANUA 'YAN UWANMU CIKIN ADDU'O'I,SABODA HALIN DASUKA TSINCI KANSU.BABU SHAKKA AKWAI TADA HANKALI MATUQA MUTUM YANAJI YANA GANI ZAMA CIKIN GARINSU YAGAGARESHI,SABODA MUMMUNAN HALIN DASUKA SAMU KANSU ACIKI NARASHIN AMINCI.
ALLAH MUNA ROQONKA DON QARFINKA DA BUWAYARKA DUK MASU HANNU ACIN JEFA BAYIN CIKIN TASHIN HANKALI DA DAMUWA ,ALLAH KAYI MAGANINSU TAHANYAR DAKASO.IDAN MASU SHIRYUWANE ALLAH KAFAHIMTAR DASU HATSARIN DASUKE CIKI KAKUMA SHIRYAR DASU.
 SANNAN MUDAI ANAN ALHAMDU LILLAH,ANAYIN ZABE(VOTING)LAFIYA,ALLAH YASA KO'INA AYI LAFIYA AGAMA LAFIYA,ALLAH KATABBATAR MANA DA ALKHAIRI,DUK WA'YANDA KAZABA MANA KATAIMAKESU WAJEN KAMANYAWA,DA ADALCI.


Friday, February 22, 2019

BABU MAGANAR SAK!!

Babu maganar sak,idan har muna son cigaba aharkar siyasa.Gobe idan Allah yakaimu za'ayi za6e,tofa sai mundawo cikin hayyacinmu munzabi wanda yakamata musamman wajen zaben "SENATOR KATSINA CENTRAL" saboda zabene tsakanin Wanda jama'a sukasani da kuma wanda ba'a sanisaniba sai wannan lokacin.
Shifa baisan jama'a ba,su ma jama'ar basu sanshiba.
Shikuwa yasan jama'a kuma alal aqalli ya amfanar da jama'a koyayane,akwai abubuwan daza'a iya gani wanda gudunmuwarsane ga al'umma.Ba ina cewa yayi duk abunda yakamata ace yayi bane,amma gaskiya yafi wanda baya jawo jama'a cikinshi.
  Nidai kam wannan shine fahimtata,kuma idan kace kudi akabani,sai kaje kacewa wanda yabaniyabani,wannan kuma ruwanka,nidai kwabo babu wanda yata6a bani dasunan,siyasa.Idan kuma akwai to sai inji.
   Shidai Dan lawan Katsina yace bashida kudin dazaiba jama'a don suza6eshi amma dai mutum yayi tunani,wallahi sak ba mafita bane wani wajenfa sai anyi angulu dakan zabo.Tunda dai koya ta bayyana gareshi APC ,PDP basa tabbatar DA nagartar dan takara,sai dai,akalli shi dan takaran.Saboda bazaiyu mumaida kanmu gida dawaba,tahanyar cewa duk dan jam'iya kaza nagartaccene ko duk dan jam'iyya kaza ba nagartacce bane.
 Mutum nawa ake yabo,ake ganin cancantarsa amma wai daya fita ya koma wata jam'iyya sai ace yazama mutumin banza,kuma barawone...,sannan mutum nawane yake cikin jam'iyyar da ake kushewa ake cewa barayine amma daya koma wata jam'iyya sai ace mutumin kirkine kuma ba 6arawo bane?
Anya akwai lissafi cikin wannan tunanin namu?,ko kuwa dai wahayi akayine duk wanda yaza6i jam'iyya ko dan jam'iyya zaka ya sa6ama Allah?
Qila kuma anyi wahayine duk wanda yaza6i jam'iyya kaza yazama yazama waliyyi duk yadda yake lalatacce?
Don haka nidai kama aza6en sanetor babu zancen sak,kuma kowa dayake katsina central yayi tunani,domin mafi alkhairin mutane shine wanda yafi amfanar dasu.
Allah yasa ayi za6e lafiya agama lafiya,Allah yazama za6in alkhairi cikin dukkan al'amuranmu,Allah duk mai so ko fatan yahaddasa fitina ko rashin gaskiya acikin za6ennan Allah ko waye/suwe Ka sansu kuma Kai kadai zaka'iya yi mana maganinsu,Allah kayi mana maganinsu tahanyar dakaso kuma kaga dama,lallai Kai mai ikone akan Komai.


Wednesday, February 20, 2019

BAZAIYIWU KOWA YASOKABA ,KAIDAI NEMI SOYAYYAR ALLAH

Idan har manzon Allah swallallahu alaihi wasallam shugaban dayafi kowa cikin halittun Allah Ta'ala:
Gaskiya,
Adalci,
Riqon amana,
Tausayi,
Hakuri,
Jarunta,
Dattako,
Son talakawa,
Iya mulki,
Iya magana,
Ilimi,
Tsoron Allah,
Son musulunci,
Son Allah dama wa'yansu nagartattun halaye ya jagoranci mutane amma ansamu fandararru dasuka bijire masa,wa'yansuma sukace azzalumine Subhaanallah!.
Toh inaga wanda bashiba,wanda arashin uwane akanyi  uwar daki.
  Aqa'idar musulunci soyayya bata hana abayyana kuskuren mutum,musamman shugaban al'umma.
 Idan ana maganar adalcin shugabanni na musulunci baza'a taba mantawada ko tsallake Khalifan musulunci na biyuba wato Umar R.A.Saboda takatsan tsan akan dukiyar al'umma Umar R.A,tayadda hatta fitilar gwamnati idan yagama aikin al'ummar dayake jagoranta kashewa yakeyi,saiya kunna tashi domin hidimarsa da iyalinsa.Saboda tausayin Umar R.A wata rana yayi nufin ba wani shugabanci,sai yayi katobara yace shi baitaba sumbatar yaransaba,sai Umar R.A yafasa bashi,yace wannan yanuna bakada tausayi dajin qai.
Lokaci bayan lokaci yana rubuta saqo zuwa gwamnoninsa yana mai gardadinsu akan akodayaushe suzama masuyin abunda yakamata,sukasance masu gaskiya,amana da adalci.Duk Wanda yasamu da zalunci dacin amana yana hukuntashi.Dabba idan tayi tuntu6e hankalin Umar R.A tashi yakeyi,saboda tsoron kar Allah yatambayeshi meyasa baigyara hanyaba har dabba ke tuntu6e.
 Allahu Akbar!! mutane nawa ke mutuwa akan hanyoyinmu saboda rashin kyawun hanya?mutane nawa suke mutuwa adalilin yunwa?mutane nawa ke mutuwa akan rashin kudin magani wanda basutaka karaba ballanta sukarya.
Amma dukda haka Umar R.A idan yana kewayawa don sanin halin da talakawansa ke ciki yanajin qorafe qorafe kala-kala da tuhuma akan baya adalci.Amma duk lokacin dayaji haka ba fada yakeba zuwa yake yaji damuwarsu yayi masu maganinta.
Saboda haka duk wanda akaji yana qorafi idan akan wanda akesone,to kar ayanke masa hukunci akan qiyayyane,a'a tayuwu duk alkhairin da'ake samu shi baije ma saba,tayiwu soyayyar dayakeyima shugaba tasa bayajin dadin yaga anshiga haqqin wani,yanajima wannan masoyinnashi nauyin dayake akansa.
 Mutum nawa kasani suna sa6awa Allah?
Mutum nawa kasani suna sa6awa umurnin Allah?,
Amma bakanuna rashin jin dadinkaba sai sai soki wanda kakeso wanda idan akabi qeqeda qeqe kafishi matsayi awajen Allah.
Akoda yaushe addu'ar alkhairi,da addu'ar shiriya sune suka kamata bakunanmu suna furtawa,amma addu'ar halaka,lalacewa basune alkhairiba koda kuwa abunda mutum yakeyi yayi muni,to farko kayi masa addu'ar shiriya,idan cutarwarsa ga al'umma ya tsananta sai ka roqi Allah yayi maganinsa tayadda shi yaso batayadda kai kakesoba.Kamar yadda Abdullahi Dan Umar R.A yabamu labarin wani hadeethi:
عن عبد الله ابن عمر-رضي الله عنهما:أنه سمع رسول الله صل الله عليه وسلم يقول إذارفعرأسه من الركوع في الركعة الأخيرة من الفجر:اللهم العن فلاناوفلانا،بعدما يقول:سمع الله لمن حمده،ربنا ولك الحمد.
وفي رواية:يدعوعلى صفوان بن أمية،وسهيل بن عمرو،و الحارث بن هشام.
فأنزل الله:ليس لك من الأمرشىءأويتوب عليهم أويعذبهم فإنهم ظالمون(ال عمران:١٢٨).
Abdullahi Dan Umar R.A,wata rana yaji manzon Allah swallallahu alaihi wasallam yana cewa bayan ya dago kansa daga ruku'i acikin araka'ar qarshe na sallar asubahi:Allah yatsinema waane,da waane,bayan yace sami'Allahu liman hamidahu,Rabbana walakal hamdu.Acin wata ruwayar yana la'antar Swafwan ibn Umayyah,da Suhailu ibn Amru,da AlHarith ibn Hishaam.
Sai Allah yasaukar da wannan aya,Al'amarinsu ba ahunnunka yakeba,ko Allah yayafe masu/yakarbi tubarsu,ko kuma yayi masu azaba,tabbas su sunyi zalunci.Ay al'amarin Allah ne kadai zai yanke masu hukunci.Kaga su 'yannanfa suna cikin shugabannin mushrikai ayaqin Uhud,Kuma manzon Allah suka yaqa harsuka karya masa haqori,yakuma la'antarsu sai Allah yadakatar dashi.Kuma sai gashi Sun musulunta.
Don Allah duk wanda akaga ya karkace to abundayafi ataimaka masa da addu'ar shiriya,idan kuma cutarwarsa tayi yawa sai aroqi Allah yayi maganinshi tahanyar dayaga dama.Allah yaqara fahimtar damu,yagafarta mana laifukanmu,yasa mugama daduniya lafiya.

Monday, February 18, 2019

KAGUJI YADA JITA-JITA

يآئيهاالذين ءامنواإن جآءكم فاسق بنبإ فتبينوا أن تصيبواقومابجهالة فتصبحوا على مافعلتم ندمين(٦).
Ma'ana:Yaa kumasu imani idan fasiqi yazo muku dawani labari akan wani ko wani abu,to kubincika(kuyi bincike kafin kuyanke hukunci ko kuma kafin kuyarda)idan bahakaba zaku aukama mutane/yanke hukunci akan jahilci,sai kuwayi gari kuna masu nadama akan abunda kuka aikata nazargin mutum ko jifanshi da abunda bai aikataba.
وسبب نزول هذه الآية:أسرول الله صل الله عليه وسلم بعث الوليد بن عقبة إ الحارث ليأخذ منهم الصدقات،وإنهم لما أتاهم الخبر فرح و او خرجوا يتلقون رسول رسول الله،وأنه لماحدث الوليد أنهم خرجوايتلقونه خاف،فرخع الوليد إلى رسول الله صل الله عليه وسلم،فقال:يا رسول الله،إن الحارث منعني الزكاةوأرادقتلي.فغضب النبي صل الله عليه وسلم عن ذلك غضبا شديدا،وهم في نفسه أنغزوهم إتاه الوفد قالوا:يا رسول الله،إسمعناأنرسولك رجع من الطريق وخشيناأن مارده كتاب جاءمنك لغضب غضبته علينا دايما نعوذ بالله من غضبه وغضب رسوله.فأنزل الله عذرهم في الكتاب.
Adunqule dalilin saukarda wannan ayar ya farune,lokacin da Manzon Allah S.A.W ya aiki Alwaleed ibn Uqbatu bn Abi Mu'aid zuwaga Al-Harith Ibn Dhirar Mahaifin Juwairiyyah uwar muminai(banul Musdalaq)yakar6o Zakka,Dasuka samu labari cewa Waleed ya taho zuwa garesu sai suka cika dafarin ciki kuma suka fito domin tarbar Dan aiken Dan aiken Allah S.A.W,to jin haka baiqarasaba sai yatsorata yana tunanin zasu cutar dashine,sai Waleed yakoma wajen manzon Allah S.A.W yake cewa manzon Allah AlHarith yahana/yaqi bayarda zakka kuma sunso kasheni dakyar nasha.Sai manzon Allah ranshi yabaci sosai har yana nufin zuwa yayaqesu,saiga baqi sunzo sukace:ya manzon Allah munji cewa dan aikenka da aiko zuwa garemu bai isoba ya koma ahanya,sai mukaji tsoro cewa kar ace mune muka 6ata masa rai,muna neman tsarin Allah daga fushinsa dakuma fushin manzonsa S.A.W sai Allah ya saukarda wannan aya.
-Abun lura yadda manzon Allah S.A.W yatasirantu da abunda aka fada masa afarko har yayi nufin daukar mataki saboda yadda da abunda aka fada masa.
-Duk nagartar mutum ba kowace magana bane idan yada za'a yadda da'itaba musamman akan laifin wani,har sai an tabbatarda gaskiyarta.
 Sannan amatsayinka na musulmin kwarai kaguji mummunan zato akan dan uwanka musulmi,domin sau dayawa sai shi Wanda ake munama zoton yabiyo masu jifarshi da magan ganun da zatone,komada laifinsane to matuqar babu maslaha to haramunne yazama abun tattaunawa.Kamar yadda Allah yafada acikin suratul Hujrat a ya ta 12:
يأيهاالذينءامنوااجتنبواكثيرامن الظن إن بعض الظن إثم،ولاتجسسواولايغتب بعضكم بعضا،أيحب أحدكم أن يأكل لحم أخيه ميت اف كرهت من هو اتقوا الله،إن الله تواب رحيم(١٢).
Ma'ana :Yaa ku masu imani kunisanci dayawa daga cikin zato ,domin lallai dayawa daga zato da'akeyi laifine,karku tsananta bincike akan sai ka gano wani yanada laifi,ko kagogama wani laifi,kuma kar dayanku yadunga gibar Dan uwansa musulmi,sai Allah yace yanzu akwai wanda zaiso yaci naman Dan uwansa bayan ya mutu,Allah yace tabbas zaku kyamaci haka,to kuji tsoron Allah tahanyar nisantar abunda yahanaku dakuma aikata abunda yayi umurni dashi,lallai Allah mai yawan karbar tubane kuma mai jinqai.
  Wannan aya mai girma tana koya mana ladabin zamantakewa tayadda bazakayita bibiyar mutumba don kakamashi da laifi,domin duk mai bin diddigi saiyakama wani da laifi to idan baidenaba shima sai Allah yajarabeshi da irin wannan laifin,abunda yafi shine kadungayi masa addu'a idan kasamu iko dagakai saishi kayi masa nasiha.
*Wata rana anzo wajen Abdullahi Dan Mas'ud R.A dawani cewa mashayin giyane har giyar tana diga agemunsa(amma ba'a ganshi yanashaba)sunanufin ayi masa hukunci.Sai Abdullahi R.A yace:mukam tabbas Allah ya hanamu tajassusi(ayitabin sawun mutum/bincike har sai ankamashi akan laifin dayakeyi nasa6on Allah),sai dai idan wani abu yabayyana afili mutum ya aikata sai muyi riqo dawannan abun daya bayyana wajen hukunta mutum(Abi Dawud:4890)
*Giba kuma manzon Allah S.A.W yace itace ka'ambaci dan uwanka musulmi dawani abu abayan idonsa Wanda idan yaji bazaiji dadiba,sai wani sahabi yatambayi Manzon Allah koda abunda yake fada yana aikatawa?sai manzon Allah yace koda abunda yake aikatawane wannan shine giba(cinnaman mutum)inkuwa baya aikatawa hakakawai ake jifanshi da abun to wannan an qagi qarya anjingina masa kenan dukkansu haramunne .
*Sai shaidar zur(shaidar qarya da zancen qarya)
قال صل الله عليه وسلم:ألا أننبئكم بأكبر الكبائر؛الإشراك بالله،وعقوق الوالدين،ألا وقول الزور،ألا وشهادة الزور،فمازال يكررها حتى قلنا:ليته سكت.
رواه البخاري
Manzon Allah S.A.W wata rana yake cewa sahabbansa :banaa fadamuku mafiya girma daga cikin manyan laifukaba?sau3 yana fadan haka,sai sukace eh ya manzon Allah kafada mana,sai yace:ayima Allah shirka,sai sa6ama iyaye(tozartasu daqin yi masu biyayya)yana kishingide agefen damarsa yafadi wa'yannan,sai yatashi yazauna yace:kusaurara da zancen qarya dakuma shedar qarya,bai gusheba yanata maimaitawa inji sahabbai har saida mukace damadai yayi shuru,saboda yadda sukaga hankalinsa ya tashi kuma yana ta sake qara maimaitawa.
-Shaidar zur shine,mutum yayi shaida akan wani abu/yafadi wata magana akan:
-abunda yasan yadda abun yake amma sai yafadeshi ba akan gaskiyar yadda yasaniba /yafaru,
-abunda baisan gaskiya ko rashin gaskiyar labariba ,amma yadunga watsashi/bada labarinsa kamar gabanshi akayi,
-abunda yasan yadda yake,sai dai anfadeshi ba tahanyar dayafaruba
Don hakadai 'yan uwa muyi takatsantsan wajen yada labari,badashi ko gaskatashi matuqar bamu dayaqini akan abunda muke fada ko ya dawadawa.
Allah yaqara tsare mu daga aikata abunda yahanemu yakuma taimakemu wajen aikata ababen dayakeso,Ya gafarta mana laifukanmu,lallaishi mai ikone akan haka.

Friday, February 15, 2019

KAKIYAYI TOZARTA MUTUM,(MUSAMMAN MUSULMI)

Kanaso kagama daduniya lafiya?
Kanaso alkhairinka ya yawaita?
Kanaso rayuwarka tayi albarka?
Kanaso adunga yima addu'ar alkhairi?
Kanaso ladarka tayawaita?
Kanaso maqiyanka suqasqanta?
Kanaso adunga yima zaton alkhairi?
Kanaso jama'a susoka?
Kanaso Allah yasoka?
Tofa babu makawa saika girmama tareda mutunta mutane aduk inda kahadu dasu,musamman musulmi,musamman dan uwanka,musamman wa'yanda kasani.
Allah dakansa yabayyana mana yadda yakarrama kuma yafifita dan Adam(mutum)akan sauran halittu,cikin fadarsa:
ولقدكرمنابني ءادم وحملناهمفي البترول بمرور ربنا هم من الطيبات وفضلناهم على كثيرممن خلقناتفضيلا(الإسراء:٧٠).
Ma'ana:Tabbas mun daraja/karrama Dan Adam kuma dirashi aka tudu(was a)da'ababen hawan da'aka hore masa,dacikin teku,kuma Allah yace munkuma azurtasu da abubuwa masu dadi,sannan muka fifitasu akan mafiyawa daga cikin abubuwan damuka halitta fifitawa.(isra'i:70).
Hakanan Luqmanul Hakim cikin nasihohin dayakema dansa da'Allah yabamu labari acikin suratul Luqman,bayan yayi mashi nasiha,akan karyayi shirka,yatsaida Sallah,yayi umurni da aiki maikyau,yayi hani daga mummuna yakumayi hakuri akan jarrabawa...,sai kuma Allah face:
ولاتصعرخدك للناس ولا ومش في الأرض مرحا،إن الله لا يحب كل مختار فخور(١٨).سورة لقمان
Ma'ana:karka juyarda kumcinka/fuskarka daga mutane danufin qasqantardasu,karkayi tafiya kana taqama,lallai Allah bayason duk wani mai gairman kai mai alfahari.
أي:لا تفعل ذلك يغضبك الله،ولهذاقال:إن الله لا يحب من كل مختار فخور،أي:مختال معجب في نفسه،فخور:أي على غيره.
Ai karka aikata ha kan,Allah zaiyi fushi dakai matuqar kana wulaqanta mutane,shiyasa Allah yace bayason maitaqama ,ai mai burge Kansas(mai jijida kai),mai alfahari gawaninsa. 
 Asuratul Isra'i haryanzu Allah yana fara:ولا ومش فى الأرض مرحبا إنك لن  تخرق الأرض ولن تبلغ الجبالطولا(٣٧).
Allah yana qara jaddadawa karkayi tafiya acikin qasa kana mai alfahari da taqama,domin duk yadda kake ganin ka kai /ka'isa bazaka iya tsaga qasaba saboda girmanka hakanan bazakai girman tsaunikaba(duwatsu manya).
عن أبي هريرة رضي الله  عنه،عن النبي صل الله عليه وسلم قال:بينمارجل يمشي فيمن كان قبلكم،وعليه بردان يتبختر فيهما،إذ خسف به الأرض،فهو يتجلجل فيها إلى يوم القيامة(البخاري:٥٧٨٩).
Abi Huraira R.A yace,manzon Allah S.A.W yace:wata rana wani mutum cikin al'ummar dasukazo kafiku,yana tafiya cikin tufafi na alfarma yana taqama acikin wannan kayan yana jiji dakai,yana raina mutane,kawai sai Allah yanitsar dashi cikin qasa ma'ana qasa qasa tatsage yafada manzon Allah yace haryanzu yana ta tafiya yana qara nitsewa har ranar alkiyama.
Hakanan Imamu Muslim ya fitarda Hadithi,:
قال رسول الله صل الله عليه وسلم:إن الله أوحى إلي أن تواضعوا،حتى لا يفخر أحد على أحد،ولا يبغى أحد على أحد.
Manzon Allah yana cewa :Allah yayi Mani wahayi dacewa kuqasqantar da kai ga 'yan uwanku musulmai,harya kasance babu wani daya dayake yima wani alfahari akan yafishi mat say I ko wata ni'ima da'Allah yayi masa,kuma  babu wani daya dayake  zaluntar wani dan uwanshi musulmi. 
Hakanan Abi Huraira bada labarin hadithin dayaji daga manzon Allah S.A.W:
أن رسول  الله صل الله عليه وسلم قال:ما تواضع أحدا لله إلا رفعه الله.رواه مسلم
Manzon Allah S.A.W yace: babu wani daya dazai qaskantar dakanshi saboda Allah faace sai Allah ya daga darajarsa.
Don haka yaakai Dan uwa Kasani awani bangare na wani had it hi,manzon Allah yana cewa ya ishi mutum sharri aranar alqiyama yaje gaban Allah yawulaqanta dan uwansa musulmi,
عن أبي هريرة رضي الله عنه،قال:قال رسول الله صل الله عليه وسلم....المسلم أخو المسلم لا يظلمه،ولا يخذله،ولا يكذبه،ولا يحقره،التقوى ههنا،بحسب امرىء من الشر:أن يحقر أخاه المسلم كل المسلم على المسلم حرام:دمه،وماله،و عرضه.
رواه مسلم.
Abi Huraira R.A yace: manzon Allah S.A.W yace:musulmi Dan uwan musulmine:
-kada yazalunceshi,
-Kada yatozartashi(yaqitaimakonsa idan yana neman taimako wajensa kuma yanada iko),
-kada yaqaryatashi/yadunga qaryata musulmi dan uwansa,
-kada yarainashi,kodan yaga Allah ya fifitashi dawata ni'ima yadauka yafishi,
Tsoron Allah anan yake,sai manzon Allah S.A.W yayi nuni zuwa qirjinsa.(tsoron Allah azuciya yace,sai gabobi sutabbatar da gaskiyar hakan ko rashin gaskiyarsa),
Sai manzon Allah yace:ya'isa yazama sharri gamutum,yawulaqanta Dan  uwansa musulmi(ma'ana ko mutum yayi abunda yakamata na ibada, bashida laifin komai amma sai yajema Allah ya qasqantar tareda wulaqanta Dan uwansa musulmi,to wanna laifin ya isa yazama sharri(bala'i)dazai jawo masa azabar Allah).
Manzon Allah yacigaba dacewa awaken kowane musulmi haramunne 
-ya zubar dajininsa,
-yataba dukiyarsa (sai dayardarsa,kuma cikin dadin rai),
-yaci/yataba/yashiga cikin mutuncinsa.
Allah yataimakemu wajen mutunta junanmu dakuma ganin qimarsu,Allah yagafarta mana laifukanmu,Allah yaba yan uwanmu marasa lafiya ,lafiya.Ameen



Wednesday, February 13, 2019

KAKIYAYE HARSHENKA👅

Dan uwa,ko kana lura/kula da abunda yake fitowa daga bakinka?
Ko kaasan Harshenka yana'iya jefaka wuta?
Ko kasan mafiyawan gabar da tafi halakar da mutum Harshene?
قال الله في محكم تنزيله:ولا تقف ماليس لك به علم إن السمع والبصر والفؤادكل أولئك كان عنه مسئولا(سورة الإسراء ٣٦).
Ma'ana ;karka bibiyi/karkafadi abunda bakada ilimi/masaniya/tabbaci akansa,kayi bincike cikin duk abunda zaka fada,saboda jinka ,daganinka dazuciyarka duk za'a tambayeka gamedasu.
قال ابن عباس:أيلا تقل،وقال العوفي:لا ترم أحدابماليس لك به علم،وقال محمد ابن الحنفية:يعني شهادة الزور،
وقال قتادة:لاتقل:رأيت ولم تر،وسمعت،ولم تسمع،وعلمت ولم تعلم،فإن الله سائلك عن ذلك كله.
وقوله:كل أولئكأولئك ،أي:هذه الصفات من السمع والبصر والفؤاد،أي:يسأل العبد عنها يوم القيامة وتسأل عنه وعما عمل فيها
-Abdullahi Dan Abbas R.A yana fada cewa ayar tana cewa karka fadi abunda bakada tabbas.
-Aufi yana fada shima akan ma'anarayar:karka jefi wani daya daga cikin mutane da wata magana da bakada cikakken ilimi akan gaskiyar al'amari
-Muhammad ibn Hanafiya yana cewa:abunda Allah ke nufi shaidar zur(Qarya),
Shikuwa Imamu Qataada cewa yayi:karkace ka gani,alhalin baka ganiba,karkace kaji,alhalin bakajiba,karkace ka sani alhalin bakasaniba,domin lallai Allah saiya tambayeka akan haka.
Ibn Kathir yana cewa akan wa'yannan siffofi,tabbas Allah zai tambayi bawa akansu ranar alkiyama,kuma suma za'a tambayesu akan wanda aka horemasu,kuma za'a tambayesu meya'aikata dasu.
وقال تعالى:مايلفظ من قول إلا لديه رقيب عتيد(ق:١٨).
Babu wata magana dawani mai magana zai furta faace akwai mala'ika atredashi yana kiyaye dukkan abunda yake fada kuma yana rubutawa.
Hakanan Allah yaja hankalinmu acikin suratul infitar:
وإن عليكم لحافظين ١٠ كراماكاتبين ١١ يعلمون ما تفعلون ١٢
Yaa kai Dan Uwa kakula kakame harshenka daga aibata mutane musamman akan abunda bakada tabbas.
  Saboda sau dayawa bawa zaiyi wata magana baya kodamuwa da maganar saboda yana hangen ai qaramar maganace amma ajefashi jahannama adalilinta.
Wata rana Abi Musa ya tambayi manzon Allah :wane musulmine yafi daraja awajen Allah,sai manzon Allah yace:shine Wanda musulmai suka kubuta daga sharrin harshensa da hannayensa.Ai baya curar da musulmai da bakinsa tahanyar yimasa:
Qarya,
Qage/QazafiQazafi,
Giba,
Annamimanci,
Da'abunda yayi kamada wيعدلها 
اعلم أنه ينبغى لكل مكلف أن يحفظ لسانه عن جميع الكلام إلا كلاما فيه المصلحة،ومتى استوى الكلام  وتركه فى المصلحة،فالسنة الإمساك عنه،لأنه قد ينجر الكلام المباح إلى حرام أو مكروه،والسلامة لا يعدلها شيء.
 Kasani Dan uwa dole akan duk wani mukallafi yakiyaye harshensa akan furta maganganu idan ba magana bane dayan akwai maslaha cikin fadanta,kuma duk lokacinda yin magana da barin yinta sukazamo dai-dai wajen maslaha, to asunnance yin shurun shiyafi,domin sau dayawa zakaga maganar dayinta ya halatta ba laifibane amma saita jawo haramun ko abunqi.Don haka babufa abunda yakamo zaman lafiya.
Allah yakiyayemu daga sharrin harsunanmu.




Sunday, February 10, 2019

SOYAYYAR ANNABI KO SUKAR ANNABI?

لقدجآءكم رسول من أنفسكم عزيز عليه ماعنتم حريص عليكم بالمؤمنين رءوف رحيم(٩:١٢٨)
Haqiqa wani irin manzo yazo muku daga cikinku,ai daga cikin jinsinku(mutunne kamar kowa tafannin halitta,ya mahaifi yanada mahaifiya,yanaci yana sha,sai Allah yafifitashi da wahayi da dabi'u nagartattu giye da kowa),duk abunda zai zama tsanani ga al'ummarsa yana damunsa matuqa,kuma mai tsananin kwadayin alkhairine gareku,kuma tabbas maitsananin tausayine da jinqai ga muminai(musulmai).
Shiyasa Allah Ta'aala ya bayyana abunda yake tabbatarda mutum yana son manzon Allah ko baya sons a,tahanyar cewa:
ومآءتاكم الرسول فخذوه ومانهاكم عنه فنتهواواتقوالله إن الله شديدالعقاب.
Na'ana;duk abunda manzon Allah yazo muku dashi to kuriqeshi,duk abunda yahaneku kuma kuhanu,kuji tsoron Allah cikin bin umurnin manzonsa,idan kuwa kukasaba masa to lallai Allah maitsananin uqubane.
وهذاشامل لأصولوالدين وفروعه وظاهره وباطنه،وأن ماجاء به الرسول يتعين على العباد،الأخذبه واتباعه،ولا تحل مخالفته.وأن نص الرسول على حكم الشيء كنص الله تعالى،لا رخصة لأحد ولاعذرله في تركه،ولا يجوزتقديم قول أحد على قو له صل الله عليه وسلم.
Wannan aya tagame asali na addinin musulunci da rasunansa,zahirinsa da badininsa(fili da boyen addini),duk abunda manzon Allah S.A.W yazo dashi dayashafi bayani akan ibaada wajine ayi riqo dashi akuma bishi,baya halatta asaa6a mass.Domin duk abunda manzon Allah yanassanta akan wani hukunci tofa kamar nassin Allah ne,saboda baya magana dason zuciya.
Don haka babu sauqi gawani daya daga cikin mutane ko uzuri agareshi yabar /yayi watsi da umurnin manzon Allah S.A.W.Kuma baya halatta(haramunne)agabaatar da maganar(umurnin)wani daya daga cikin mutane akan maganar manzon Allah S.A.W.
Hadeethi ya tabbata daga Abi Hurairah R.A cewa; manzo S.A.W yace:Idan na'umurceku dawani al'amari to kuzodashi(kuyishi)gwargwadon ikonku,kuma abundana haneku gameda aikatashi kunisanceshi.(Bukharin 7288)
أذاأمرتكم بأمروفأتوامنه ما استطعت مزز و ما نهيتكم عنه فاجتنبوه.
Shiyasa ko soyayya bakasamun masuson Manzon Allah dagaske sunason Wanda bayason Allah da Manzonsa,kamar yadda Allah Ta'ala yafada acikin littafinsa  sura ta 58 ayata 22  
لاتجدقوما يؤمنون بالله واليوم الأخريوآدون من حآدالله ورسوله ولوكانواءبآءهم أوأبنآءهم أوإخوانهم أوعشيرتهم....
Ma'ana bakata6a samun wa'yansu mutane dadukayi imanida Allah kuma sukayi imani daranar qarshe,suna qaunar wanda bayason Allah bayason manzonsa,wannan mutumin kowa koda iyayensane,ko 'ya'yansa,ko 'yan uwansa ko danginsa......
 Fadin ina son manzon Allah dabaki kadai bazai isa mutum yakasance masoyinsa da Allah yake nufiba har sai akinsa yayi dai-dai dakarantar warsa.Sai duk wata ibada dazakayi tayi dai-dai dayadda manzon Allah yace ayita/yyayita.
 Saboda kyawun ibadarka Allah bazai kar6etaba matuqar babu kwaikwayon manzon Allah.Allah Ta'ala ya fada cewa idan kuka bishi tabbas kunshiryu.
Hakanan cikin suratu Al-Imran ayata 31 Allah yana qalubalantar Wanda sukace baruwansu dabin manzon Allah dacewa;
قل إن كنتم تحبون الله فاتبعوني يحببكم الله ويغفرلكم ذنوبكم والله غفور الرحيم(٣١).
قل أطيعوا الله والرسول،فإن تولوافإن الله لا يحب الكافرين(٣٢).
Allah yace: kafada musu ya kai manzon Allah indai har dagaske kuna son Allah to kubini(kubi manzon Allah)idan kuka bini sai Allah yasoku kuma idan yasoku zai gaafarta muku zunubanku.(31)
Daya ayar kuma Allah yace:Kafada musu subi Allah subi manzonsa,inkuwa suka juya baya sukaqi bin Allah da manzonsa ,to lallai Allah bayason mutane kafirai.
Don cikkiyar soyayyar manzon Allah itace biyayya gareshi cikin duk abunda yazo dashi,yakuma qyamaci duk abunda manzon Allah yaqyamata kuma yahana.koda ranka yana son abu matuqar manzon Allah yahanashi to zaman lafiyanka kaguji wannan abun,koda zaka 6ata damutane,idan kuwa yace ayi abu koranka bayaso sai haqurtar dazuciyarka kabi umurninsa domin hakanne tsira agareka duniya dalahira.
Allah yaqara azurtamu dabin shiriyar manzon Allah S.A.W,
Allah yatausaya mana yagafarta mana laifukanmu,
Allah yarufa mana asiri duniya dalahira

Saturday, February 9, 2019

أمهات المؤمنين(٢)

                       سودةبنت زمعة
هي أم المؤمنين سودة بنت زمعة بن قيس القرشية،وهي أول من تزوج بها النبي بعد خديجة.
وكانت سيدة جليلة نبيلة،وكانت أولا عند السكران بن عمرو،وهاجرت معه إلى الحبشة،فأغضبت أهلها بهجرتها،ولما عادت من هجرتها توفي زوجها رحمه الله ولما توفي خلف زوجته(أي سودة) من غير ناصر،ولا عائل،فتزوجها النبي صل الله عليه وسلم،وكانت في الخامسةوالخمسين من عمرها
Saudatu diyar zam'ah dan Qais baquraishiya,itace farkon matar da manzon Allah S.A.W ya'aura bayan rasuwar Khadijah R.A.Takasance macen kirki mai halayen nagartattu.Dafarko ta auri Sukraan Dan Amru,kuma tayi hijira tareda mijinta zuwa Habasha,wanda har hakan yajayo danginta sukayi fushi da'ita akan hijirar datayi.lokacindata dawo daga hijira sai mijinta yarasu.Alokacin dayarasu sai yabar  matarsa (Saudatu R.A)batada wani wanda yake taimakonta,yake kulawa da hidimominta nayauda kullum.
Ganin haka,sai annabi S.A.W ya aureta.Shiyasa dayawa daga cikin magabata tundaga Sahabbai Allah yaqara yarda dasu sukan auri mace(bazawara)don dauke mata wahalar rayuwa,domin duk bazawara tasaba agidan mijinta shiyake kulawa da ita,yake bata abinci,abunsha,sutura,sabulun wanka dana wanki harma dakudin kashewa.To dazarar tarabu damintafa sai wa'yannan abubuwa suyi mata wuya,shiya musulunci yayi albishir mai tsoka ga wanda yake taimakawa bazawara,gudun karta Shiga wata hanya don neman abunda zata rayu.
  Itama Saudatu R.A saboda kwadayin zama damanzon Allah yasa tacema A'isha R.A ta bata kwanakinta(idan manzon Allah yana dakin Saudatu R.A to dakin A'isha zaice)saboda wata rana dawani abu yafaru,cema Manzon Allah tayi ina hadaka da wanda yasaukar maka da littafi karka sakeni,saboda tsufana banida buqatar namiji yanzu,sai dai in a so atasheni ranar qiyama cikin matanka,sai manzon Allah yadawo da Saudatu R.A.
khalifancinA'isha R.A takecewa babu macen danikeso kamar Saudatu R.A.ta rasu alokacin khalifancin Umar R.A.

Friday, February 8, 2019

أمهات المؤمنين(١)IYAYEN MUMINA

      خديجة بنت خويلد 
أم المؤمنين ،خير نساء العالمين ،أم القاسم ابنةخويلد،وأم أولاد النبي صل الله عليه وسلام.وأول من آمن وصدقه قبل كل أحد 
وهي ممن كمل من النساء ،كانت عاقلة منسوبة بالكرم،من أهل الجنة.
Uwar muminai ,mafi alkhairin mata,mahaifiyar Qaasim diyar Kuwailid,kuma itace mahaifiyar duka 'ya'yan manzon Allah S.A.W.
Kuma itace farkon wadda tayi imani kafin kowane mutum,ana siffantaatada karamci.
Tana daga cikin mata da'akayi atarihin duniya masu cikar kamaala,kuma yar aljannah,kamar yadda manzon Allah S.A.W yafada:
قال أبي هريرة رضي الله عنهأتى جبريل النبي صل الله عليه وسلم فقال:يا رسول الله! هذه خديجة قد أتت معها إناء فيه طعام أوشراب،فإذا هي أتتك فاقرأ عليها السلام من ربهاومني،وبشرها ببيت في الجنة من قصب،لا صخب فيه  ولانصب.
صحيح البخار(٣٨٢٠).
Abi Hurairah R.A yace :malaa'ika Jubreelu yazo wajen annabi S.A.W sai yace:yaa manzon Allah S.A.W ! ga Khadijah R.A nan tafe zuwa wajenka,atare da ita akwai kwano cikinsa akwai abinci/abunsha,idan ta'iso wajenka kakaranta mata sallama daga Ubanhinta dakuma ni,sannan kayi mata albishir dawani irin gida acikin aljannah wanda babu hayaniya babu tashin hankali .
 Wannanfa Itace Khadijah Allah ya aiko mala'ika cewa Allah yana gaisheta shima kuma Jubreelu A.S yana gaisheta da kuma tabbacin gida acikin aljannah.
Yana daga karamarta Manzon Allah S.A.W itace matar dayafara aure,kuma bayan ya aureta bai hadata wata mataba tsawon she kara 25 har saida rasu sannan ,kuma dukkan 'ya'yansa S.A.W ita tahaifesu.
Ta taimaki manzon Allah da dukiyarta batareda tanayi masa goriba akan duk abunda tayi masa ko tab as a,tana qarfafa masa guiwa akan harkar da'awarsa kamar yadda yazo lokacin da akafara yimasa wahayi ya firgita amma ita tadunga kwantar masa da hankali cewa wallahi Allah bazai tazartaakaba,saboda kana sadarda zumunci,kuma kana dagaskiya wajen ma gana(baka fadin qarya)kana girmama baaqo,kana taimakon gaskiya.
Haka akeso kema kikasance awajen mijinki,saisai yadunga alfahari dake .manzon Allah kobayan da Khajijah tarasu yana girmamawa tareda mutunta Qawayenta.
Ta rasu kafin hijira da shekara 3,har Aisha wata rana manzon Allah ya'ambaci Khadijah,sai dan kishinnan namata yamotsa tace tsowar kullum kake magana,ai Allah ya canza maka wa'yanda suka fita,sai yace Allah bai canzamin wanda suka fitaba domin itafa;
Tayi imani dani lokacinda mutane suka kafirce Mani,
Tayi mushaaraka dani cikin dukiyarta lokacin damutane suka hanani tasu dukiyar,
Kuma Allah ya azurtani da 'ya'ya da'ita,baibani watantaba,sai A'isha R.A tace gaskiya bazan sake magana akantaba (sabodata fahimci mat say in ta)
Manzon Allah idan yayanka akuya yana aikawa qawayen Khadija R.A,har wata rana akayi mashi magana akan hakan,sai yace ai ina son mai sonta shiyasa nake aika masu.
Allah yaqara mana son matan manzon Allah S.A.W(iyayen muminai)

Tuesday, February 5, 2019

MENENE MATSAYIN MASU KAFIRTA SAHABBAI?

Ko shakka babu duk duk wanda yajefa kansa cikin layin masu zagi dacin mutuncin sahabban Manson Allah S.A.W to wannan Iran kana neman halakakke to ka saamu.
 Saboda duk mai aibatasu,to tabbas yana qaryata Allah kaitsaye yana kuma qaryata manzon Allah S.A.W.,Allah ya tabbatarda ya yarda dasu kuma suma sun yarda da Allah
قال الله في تعالى:لقد رضي والله عن المهاجرين والأنصار والذين التبعواهم بإحسان.....
Haqiqa Allah ya yarda da muhaajirun(mutanen makka) da ansaar(mutanen madina) da wa'yanda sukabisu dakyautatawa.
Shin muhajirun da ansaar suwa Allah yake nufi?
Ko kuwa da wa'yansu mutanen damuke rayuwa dasu sune muhajirun da Ansaar?
Ko kuwa masu zagin A'isha R.A su ake nufi?
Kai !!!mai zagin sahabbai idan kana neman rahamar Allah to ka bi dokokinsa kayarda da nagartar sahabbai.
  Anya son da kakewa manzon Allah S.A.W nagasskiya ne?
Anya ba manzon Allah kake zagiba?
Domin duk idan kanaso kagane mutum nakirkine ko nabanza to kabinciki suwaye abokansa.
Watarana manzon Allah S.A.W ya hau dutsen uhud tareda wasu sahabbansa ,ga abun dayafaru:
عن أنس رضي الله عنه قال:صعد النبي صل الله عليه وسلم أحدا،ومعه أبو بكر وعمر  وعثمان،فرجف وقال:اسكن أحد فليس عليك إلا نبي  وصديق وشهيدان.
صحيح البخاري)٣٦٩٩)
Anas R.A yace:manzon Allah ya hau saman dutsen uhud a watarana,atare dashi saman dutsen akwai Abubakar siddeeq R.A,da Umar R.A,da Uthman R.A,sai dutsen yayi motsi kamar zai fado dasu sai Manzon Allah yace kai uhud kanatsu ha wa'yansu mutane bane asamanka illa Annabin Allah,Siddeeq dakuma Shaheedai guda biyu.
Sahihul Bukharin(3699)
 Haba mai zagin sahabbai ina hankalinka yake ina wayonkawayonka?Tunda har dutsi ana sanar dashi matsayi da darajar wa'yanda suke samanshi.kuma yashiga hankqlinsa,amma kai dutse ya fika hankali kenan?
Allah yaqara datar damu Allah yahadamu da sahabbai manzon Allah acikin Aljannah

Saturday, February 2, 2019

MAATA KUKIYAYE AMANAR ALLAH!!!!

قال الله تعالى:وقرن في بيوتكم ولا تبرجن تبرج الجاهلية الأولى،
الأحزاب٣٣
Allah Ta'ala yaa fara:kutabbata acikin gidajenku na karkuyi fitar tabarruji irin tabarrujin jahiliyyar farko.Ahzaab 33.
قال ابن كثير رحمه الله في تفسير هذه الآية:
أي؛ألزمن بيوتكم فلا تخرجن لغير حاجة،ومن الحوائج الشرعية.
Ibn Katheer ya fada acikin tafseerinsa acikin ma'anar wanna ayar:
Ay;kulazimci gidaajenku karku fita ba tareda wata buqaataba ta dole,dakuma buqaatu irinna shari'ar islaama.
تعريف التبرج :هو أن تظهر المرأة للرجل الأجانب الذين ليسوا من محارمها ما يوجب عليها الشرع أن تستر من زينتهاومحاسنها.
Ma'anar tabarruj:shine mace tabayyana abunda shari'a ta wajabta/shar'ant suturcewa/rufewa na kwalliyarta da kyayun jikinta ga ajnabi wanda ba muharramintaba.
التبرج للمرأة لها ثلاث معاني:
١-أن تبدي للأجانب جمال وجهها ومفاتن جسدها.
٢-أن تبدي لهم محاسن ملابسها وخليها.
٣-أن تبدي لهم نفسها بمشيتها وعملي له انت بناتها.
Tabarruji ga mace yana daukar ma'ana uku(3)
1-shine mace tabayyana kyawun fuskarta da bangaren dayake daukar hankalin maza ajikinta(yake fitinar da maza)ga ajnabinta(wandaba muharramintaba.
2-Mace tabayyana musu(maza)kyawawan tufafin data sanya ajikinta da kayan adonta(sarqa,'yan kunne,zobe da makamantansu)
3-Mace tabayyana musu(mazan)kanta tahanyar tafiyarta da rangwada da kuma sanya turare mai qamshi.
Yaa ke 'yar uwa mumina,kidaure kikatange kanki daga halaka tahanyar zama acikin gida,idan kuwa fita ta kaamaki to kifita cikin shiga irin ta shari'a
   Kuma arage yawan magana da mazanda daba muharramaiba domin shi ma ana lissafashi acikin tabarruji.
Saboda duk lokacin da'aka kika yawaita magana da namijindaba muharraminkiba shaquwace zata biyo baya.Idan maganar aurene wannan babu laifi haka akaso,amma idan kina da aure to kinga anshiga cikin sabon Allah.
Allah yaqara tsare mana imaninmu,yakuma gaafartaa mana zunubanmu baadan halinmuba.

Friday, February 1, 2019

AIKO MANZON ALLAH

Allah Ta'ala ya aiko annabi Muhammad S.A.W dasaqon yadda yakeson abauta masa(Allah).shiyasa Allah yaqalubalanci masu riyawa cewa suna son Allah amma bazasubi manzon Allah ba;Allah yana fada acikin Al'Imran :
قل إنكنتم تحبون الله فاتبعوني يحببكم الله ويغفر لكم ذنوابكم والله غفوارالرحيم
Ma'ana:indai hardagaske kuke kuna son Allah toh kubini(manzon Allah),sai Allah yasoku,kuma zai gaafartaa muku zunubanku,lallai Allah mai gafarane kuma maijin qai.
 Kuma Hadeethi ya tabbata daga Mansonmanzon Allah S.A.W,
قال رسول الله صل الله عليه وسلم:ما بعث الله نبي إلا كان حقا عليه أن يدل أمةه على خير ما يعلمه لهم.
رواه مسلم
Manzon Allah S.A.W have:babu wani annabi da Allah zai aiko faace ya zama haqqine akansa ya nunama mutanensa duk wani alkhairi,awata ruyawar da kuma duk wani sharri.
Shiyasa wani babban sahabi (Huzaifa ibn Yamaan R.A) yakecewa:
Duk wata ibaada da sahabban manzon Allah basuyitaba ,toh kada kuyita,domin su'yan farko basubarma naqarshe wani abun cewaba dangane da add inaddini faace saidasukayi magana akai.
Saboda haka soyayyar manzon Allah bakawai furuci bane da baki,a'a yimasa biyayya shine haqeeqanin ssonsa.wani mai hikima yana cewa:
لو كان حبك صادقا لأطعته   إنالمحب لمن يحب مطيع
Ma'ana :Da'ace son da kakewa manzon Allah nagaskiyane da kaayi masa biyayya   domin maso ysnayima abun dayakeso biyayya.
Allah yafaafarta mana laifukanmu yacire mana son saaba masa,Ameen