Friday, February 22, 2019

BABU MAGANAR SAK!!

Babu maganar sak,idan har muna son cigaba aharkar siyasa.Gobe idan Allah yakaimu za'ayi za6e,tofa sai mundawo cikin hayyacinmu munzabi wanda yakamata musamman wajen zaben "SENATOR KATSINA CENTRAL" saboda zabene tsakanin Wanda jama'a sukasani da kuma wanda ba'a sanisaniba sai wannan lokacin.
Shifa baisan jama'a ba,su ma jama'ar basu sanshiba.
Shikuwa yasan jama'a kuma alal aqalli ya amfanar da jama'a koyayane,akwai abubuwan daza'a iya gani wanda gudunmuwarsane ga al'umma.Ba ina cewa yayi duk abunda yakamata ace yayi bane,amma gaskiya yafi wanda baya jawo jama'a cikinshi.
  Nidai kam wannan shine fahimtata,kuma idan kace kudi akabani,sai kaje kacewa wanda yabaniyabani,wannan kuma ruwanka,nidai kwabo babu wanda yata6a bani dasunan,siyasa.Idan kuma akwai to sai inji.
   Shidai Dan lawan Katsina yace bashida kudin dazaiba jama'a don suza6eshi amma dai mutum yayi tunani,wallahi sak ba mafita bane wani wajenfa sai anyi angulu dakan zabo.Tunda dai koya ta bayyana gareshi APC ,PDP basa tabbatar DA nagartar dan takara,sai dai,akalli shi dan takaran.Saboda bazaiyu mumaida kanmu gida dawaba,tahanyar cewa duk dan jam'iya kaza nagartaccene ko duk dan jam'iyya kaza ba nagartacce bane.
 Mutum nawa ake yabo,ake ganin cancantarsa amma wai daya fita ya koma wata jam'iyya sai ace yazama mutumin banza,kuma barawone...,sannan mutum nawane yake cikin jam'iyyar da ake kushewa ake cewa barayine amma daya koma wata jam'iyya sai ace mutumin kirkine kuma ba 6arawo bane?
Anya akwai lissafi cikin wannan tunanin namu?,ko kuwa dai wahayi akayine duk wanda yaza6i jam'iyya ko dan jam'iyya zaka ya sa6ama Allah?
Qila kuma anyi wahayine duk wanda yaza6i jam'iyya kaza yazama yazama waliyyi duk yadda yake lalatacce?
Don haka nidai kama aza6en sanetor babu zancen sak,kuma kowa dayake katsina central yayi tunani,domin mafi alkhairin mutane shine wanda yafi amfanar dasu.
Allah yasa ayi za6e lafiya agama lafiya,Allah yazama za6in alkhairi cikin dukkan al'amuranmu,Allah duk mai so ko fatan yahaddasa fitina ko rashin gaskiya acikin za6ennan Allah ko waye/suwe Ka sansu kuma Kai kadai zaka'iya yi mana maganinsu,Allah kayi mana maganinsu tahanyar dakaso kuma kaga dama,lallai Kai mai ikone akan Komai.


0 comments:

Post a Comment