Monday, March 11, 2019

DAGA QIN GASKIYA SAI BATA!!!!

Sau dayawa idan mu yana rufewa tayadda sai ayi rashin gaskiya amma kuma maimakon wanda yayi rashin gaskiya abashi rashin gaskiyarsa sai aqirqiro wata qa'aida dandai atabbatar darashin gaskiya.
 Kamar yadda kowa yake bibiyan zabe/sakamakon zaben Kano ansan duk abunda yake faruwa har irin mummunan laifin dawani babban jami'in gwamnati yatafka wanda inda umurni za'abi kamar yadda shugaban kasa yabayyana da yayita rayuwarsa.Amma amaimakon wannan aika aika yazama abunda zai tabbatarda kasawa ta jam'iyya mai mulki a kano sai laifin yazama matakin dazai qara basu damar shirya abunda suke shirin shiryawa.
 Shifa mai abun fada baya fada,idan kuma har jam'iyyar adawa zatayi magudi amma babu wanda zai gane laifin da akayi sai "deputy Governor" to lallai akwai lauje cikin nadi.Idan kuma har amatsayinshi na mataimakin gwamna yaga wani rashin gaskiya da'akayi sai mutambayi kawunanmu:
-Ya kamata yazo yakwashe result dindin/votes?
-Ya kamata ahukunta wanda bashi yayi laifiba dalaifin marar gaskiya?
-Magana yakamata yayima wanda alhakin abun yake awuyansu ko kuwa shi doka tace yadauki mataki dakansa?
-Sannan meyatsayar dasakamakon haka har zuwa wannan lokacin?
-meke tunanin mutane idan dan jam'iyyar adawane yayi wannan katobarar?
-Anya anason kamanta adalci kuwa?
Komadai menene ita gaskita dayace tak daga kinta kuma sai bats.baikamata ace jagorori sune ke hura/rura wutar da zata iya janyo tashin hankaliba atsakanin mutanen da ake jagoranta.
Allah Ta'ala yana fada cewa kada qiyayya tasaku kuqi yin adalci/kin fadin gaskiya/aikata gaskiyarba,Allah yace kuyi adalci shine yafi kusada tsoron Allah.
Sannan Allah yace kufadi gaskiya koda akan kankune kowa'yansu nakusa daku.Saboda haka indai don al'umma akeyi to bai kamata abunda al'ummar suka zaba ahanasuba KO kuma ayi qoqarin kwace masuba.Kuma lallai yakamata wanda akejin maganarsa yayi magana tun kafin al'amari ya runcabe,wannan shine dattako kuma shine,adalci sannan kuma shine riqon amana.Daman shi adalci shine ajiye komai inda yakamata.
Nidai kam dukda ba masanin sha'ar qasa bane amma tunanina ya bani cewa it ita inec wuqa da nama duk ahannunta take,duk wani rashin adalci daza'ayi tofa idan Inec bata bayarda hadinkaiba bazai yiwuba.Don haka cewa asake yin zabe nanda sati uku masu zuwa a Nasarawa tabbas bashine hangar dayakamta abiba,saboda kenan shi mailaifi yasamu yadda yakeso kenan,mafi sharrin shugaba shine wanda mutanen dayake jagoranta bash sonshi amma shi yacije saiya mulkesu.
Kuma babu jam'iyyar idan akaqi zabanta ansabama Allah ba,indai batareda wani daliliba.Inec Kuji tsoron Allah karku jefa al'ummar Kano cikin rudanifa.Allah yakyauta yataimaki wanda al'umma keso kuma shima idan yaci Allah yabashi ikon kyautata masu kamar yadda suka bashi daman yajagorancesu.Itadai karya fure takeyi bata 'ya'ya.
GASKIYA MAI DACI!!GASKIYA MAI DACI!!

0 comments:

Post a Comment