Tuesday, March 12, 2019

SUGABANCIN QASATA NIGERIA

 Kai talakan Nigeria wallahi yakamata kadawo hayyacinka,dangane da qoqarin ganin ka 6ata ma wani rai akan shuwagabannin da mafi yawa batakai sukeba.Ko addini kakeyi don ka6atama wani rai to bakada lada.Amma abun mamaki dayawa daga cikin talakawa idonmu ya rufe akan wani wanda wallahi idan za'a rasaka bazaiji ko ajikinsa ballantana yaji damuwa indai har rasaka zaisa yacimma manufarsa.
 Abun mamaki wani lokacin saikaga harda malamanmu,basu auna maganganun dasuke furtawa akan siyasa dakuma Dan siyasar Nigeria.Tayadda zakaga/zakaji malami yana fadin maganganunda mai ilimin addini kuma akan fahimtar magabata nakwarai baikamata yana yinsu.Bayan duk ta bayyana babu irin rashin gaskiyarda kiwane Dan jam'iyya bayayi hasalima mafiyawan wa'yanda ake tsarkakewa abunda yayisu shiyayi wa'yanda ake zagi.
Ni haryanzu abunda kasa yarda dashi shine duk cewa duk Dan jam'iyyar su wane duk lalacewarsa,duk rashin gaskiyarsa indai Dan jam'iyyajam'iyyar wanene/suwane mutumin banzane.Shikuwa wanda baya cikin jam'iyyar suwane koda ya fi Dan jam'iyyarsu wane nagarta.
Nidai abunda nasani wanda yake saman mulki yafi damar yin magudi sama da wanda yake bashida mulki.
Kuma indai gaskiya da adalci za'ayi mutum bazai dage ala dole saiya zarce kuma kotawane hanya.
Amma tabbas yakamata mudawo mufuskanci gaskiya,babu laifi kayautatama mutum zato kuma dunga yabonshi akan kyawawan halayensa,amma hakan bai bude kofar shiga gaban Allah da manzonsaba,wajen magana da aiki kamar yadda Allah Ta'ala yafada acikin littafinsa mai tsarki:
يأيها الذين أمنواولا تقدموابين يدي الله ورسوله واتقوا الله،إن الله سميع عليم(١).
Allah ya fada cewa:ya ku wa'yanda kukayi imani(kuka bada gasikiya da Allah),karku shiga gaban Allah damanzonsa akan wajen furta wani abu aikata wani aiki acikin addinin musulunci,kuji tsoron Allah lallai Allah mai jine akan duk abunda kuke furtawa kuma mai cikakken ilimi akan duk abunda bayinsa suke aikatawa afili da boye.
 Don haka lallai mudinga taka tsan-tsan akan tsarkake kawunanmu,Domin shi Allah shikadaine yasan abundake fili da 6oye,masanin abun dayake cikin zukatan bayinsa.Tabbas akwai nagartattu acikinmu amma abudake namu shine mukyautata masu zato,tahanyar cewa da'alama wane waliyin Allah ne,tahanyar la'akarida halayen waliyyai dayakedasu cikin irin siffofinda Allah ya fada ko manzonsa S.A.W.Amma sai kaji wani harmada rantsuwa cewa wane waliyyine.Maimakon yace Wallahi duk wanda yasiffantu da siffofin waliyyai da Allah yabayyana ko manzonsa ,Wallahi waliyyine.Allah ya fada awani bangaren ayata 32 cikin suratul Najmi
فلا تزكوا أنفسكم،هو أعلم بمن اتقى.
Allah yana cewa karku tsarkake kawunanku shi Allah shine mafi sanin maijin tsoransa.
 Kawai ayi gaskiya aba jama'a wanda suka za6a,tundadai ba wahayi akayiba akan dole sai dan jam'iyya kaza yaci za'a bada mulki,shikuma dan jam'iyyar adawa idan yaci sai ayi amfanida "inconclusive ".
 . Wai anmaida shugabanci business din dayafi tara/kawo kudi masu yawa.
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'OUN!!!

0 comments:

Post a Comment