Friday, March 15, 2019

MANZON ALLAH (S.A.W)KADAI AKEBI IDO RUFE!!!

Wallahil Azeem!!:Allah bazai tambayekaba idan bakabi,malam waneba,ko shehi waneba sannan bazai kamaka dalaifiba idan baka shiga kungiyar Izala ko Dariqa ba.
Amma tabbas Allah zai tambayeka tareda azabtarwa maitsanani idan bakabi manzon daya'aiko makaba,Muhammad swallallahu Alaihi was all am.Sannan kuma Allah zai kaamaka dalaifi idan kaqibin Qungiyar Sahabban Manzon Allah Swallallahu alaihi was all am.
Saboda duk duniya babu wanda Allah ya'aiko maka,wanda kuma dole awajensa zaka koyi addini irin kuma kafahimceshi,kuma idan kayi aikin Allah yakar6a sai Annabin Allah kuma manzonsa Muhammad Swallallahu alaihi wasallam.
قال الله تعالى:هواالذي أرسل رسوله بالهدىودين 
لحق ليظهره على الدين كله وكفى بالله شهيدا(٢٨)
محمد الرسول الله،والذين معه أشدآء على الكفار رحماء بينهم.....(٢٩)
Allah Ta'ala yana fada acikin suratul Fathi ayata 28-29 cewa:Allwh shine wanda ya'aiko manzonsa Annabi Muhammad S.A.W dashiriya dakuma addinin gaskiya(musulunci)don yarinjayarshi akan duk wani addinin dabashiba kuma lallai Allah ya'isa yazama maisheda akan hakan.
 Muhammadu Manzon Allah ne(Allah yana shedawa duniya akan masu qaryata manzoncin annabi S.A.W ,ko sunqi ko sunso Allah ya tabbatar dakasancewarshi manzonsa,wanda yazo dasaqon addinin musulunci )wa'yanda suke taredashi(sahabbansa)basu jiyar dakafirai dadi,basu sassauta mash,amma suna jinqan junansu suna tausayin junansu(suna taimakama junansu,basuson abunda zai jefa 'yan uwansu cikin halin qaqanikayi.......
Duk duniya Manzon Allah kadaine yakamata yazama madubi awajenka ,duk bunqasar malami ana binshine idan abunda yake fada ko yake koya mana yayi dai-daida karantarwar manzon Allah S.A.W.
   Saboda shikadaine binsa yake addini sa6a masa kuma yake jawoma mutum fushin Allah,kamar yadda Allah yatabbatar manada haka,cikin suratu Noor ayata 63
فليحذر الذين يخالفون عن أمره أن نصيبهم فتنة أويصيبهم عذ اب أليم
Masu sa6a umurnin manzon Allah suji  tsoron fitina sakamakon sa6a masa,ko kuma wata azaba mai radadi.
قال الله تعالى:من يطع الرسول فقد أطاع الله و من تولى فما أرسلناك عليهم حفيظا
Duk wanda yayimaka biyayya to tabbas Allah yayimawa,.....
وقال تعالى:وما ءاتاكم الرسول فخذوه ومانهاكم عنه فانتهوا،والتقوا الله،إن الله شديد العقاب(الحشر:٧)
Duk abunda manzon Allah S.A
.W yakawo muku/ya umurceku tokuriqeshi dakyau,sannan duk abunda yahaneku akansa to kuhanu daga aikatashi,kuji tsoron Allah,lallai Allah mai tsananin uqubane akan masu sa6ama umurnin manzon Allah
Kaf duniyar nan babu Wanda akaba saqon addinin musulunci sai manzon Allah,kuma ya'isar dasaqon Allah.
Wallahi babu wani abu acikin addini da idan aka aikatashi za'asamu lada fache saida manzon Allah yayi bayaninsa.
ADDININ ALLAH YAGAMA CIKA TUNKAFIN MANZON ALLAH YABAR DUNIYA,ALLAH YATABBATAR DAHAKAN.
Kuma dole saikayi Ibada yadda manzon Allah S.A.W yayi sannan zaka samu ladar abunda kayi wajen Allah.
Muhadu arubutu nagaba;Ba malam,wane,ko shehi wane aka aiko makaba.
Allah yadatardamu dabin sunnar manzon Allah  S.A.W.


0 comments:

Post a Comment