صدق رسول الله صل الله عليه وسل إذقال:أخوف ما أخف على أمتي الأئمة المضلون.
Tabbas manzon Allah yayi gaskiya ,domin yafada cewa:abunda nafijima al' ummata tsoronsa shine jagorori batacci/batattu.
Abunda nalura dashi a Nigeria:
*Musulmi bashida 'yancin magana
*Jami'an tsaro na DSS sun kware wajen kama malaman addinin musulunci
*Ba'ason malamin addini yakasance yana fadin gaskiya ,sai dai rufa-rufa
*Amfison malaman da suke yaqar 'yan uwansu saboda wata jam'iyyar da 80 % zuwa 90% 'yan jam'iyyar da'ake iqirarin bata masu gaskiya bace
*Anfison ana kashe 'yan uwanka kace gyara ake
*Anfi taimakon addininda ba musulunciba
*akullum ba'aso Dan kasa yasan inda ake ha'intarshi
*Jami'an tsaro sunzama karnukan farautar masu mulki
*aduk lokacinda kaji ance ankama wani saboda maganar dayayi domin tana iya jawo rikici, to zakaga musulmine
*Manyan malamai dayawa daga cikinsu sunkoma neman gamsarda masu mulki saboda maslaharsu kadai
Iyakar sanina babu malamin sunnah dayake zuga mutane suyi ta'addanci.
Duk abunda malami zai fada kodai yayi gaskiya kokuma yafadi akasin haka.Sai aduba maganarsa idan gaskiya yafada sai adauki maganarsa domin ayi gyara,idan kuma ba gaskiya bane sai warware maganarsa da hujjoji masu gamsarwa.
Mu abunda muke cewa wa'yannan abubuwan dake faruwa na kashe-kashe rayukan al'umma batareda laifin komaiba sai dan suna musulmai,da agwamnatin bayane wa'yanda suke hana afadi zahirin abunda yake faruwa sunefa suke kuka suna tir da Allah wadai da abunda yake faruwa.
Sai yanzu kuma sai ace abunda yake faruwa baza'ayi maganaba.
Kai mukam mungaji da gafara sa bamuga Qahoba.
Allah Muna tawassuli da ibadar azumi damukeyi,karatul al'qur'ani dasuran ibadu Kaku6utarda bayinka da'aka tsare abisa zalunci,Allah katsare yan uwa musulmi aduk inda duke.Allah kagyara mana shuwagabanninmu.Idan kuma ba masu shir yuwa bane kadaukar mana matakin daya dace akansu.AMEEN
0 comments:
Post a Comment