Azahirin gaskiya akwai matsalolin da alokacin baya basu tsananta kamar yadda ake shan wahala yanzuba
Farkodai yakamata dukkanmu musani cewa tabbas komai yana kasancewane bisa qaddarawar Allah.Idan Allah yaso faruwar abu yana kasancewa kamar yadda yaso batareda gudummuwar kowaba.
Amma hakan baya nuni dacewa duk abunda shuwagabanni sukayi nakuskure sai ace ai haka Allah yaso babu mai iya kawo sauqi sai Allah.Abbas hakane amma;
menene hikimar hukunta shugabanci?ko shakka babu don maslahar al'ummane.Kai shugaba dole kasani cewa talakawa nada haqqi dayawa akanka,na daga cikin haqqokin:
*tsare masu lafiyarsu,
*Tsare masu dukiyoyinsu,
*tsare masu addininsu,
*Samar da walwala acikinsu,
*Samar masu abunda yake buqtuwane na doke,
Kamar samarda ruwansha,wutan lantarki,samarda magunguna da kulada asibitocin.
Amma kash!!! Al'amarin yanada bantsoro.Azumi al'ummar musulmai sukeyi amma ruwan jarka da'ake saye yayi wahala,da kudinka kan a so kasaya babu ruwan.
Yanzu haka danike rubutunnan munyi awa saba'in da biyu(72 hours)babu wutan lantarki,adai dai lokacin da shuwagabanni basusan da matsalar wuta ko ruwa ba.Tabbas shugabanci ba abu bane mai sauqi,ammafa su sukanema kuma wallahi dukkansu dadin mulkinnan sukeji,abunda yadami talakawa su ba matsalarsubace.
Wannan wani irin canjine?
Anya kuwa masu kare shuwaganni acikin kuskure idan sunyi zasu'iya fuskantar Allah domin bada kariya akan quncin rayuwa da talaka yashiga adalilin sakaci ko nuna halin ko'inkula da shuwagabanni suke nunawa?
Koda yake nidai nagama nazari akan shuwagabanninmu,akwai wanda mune ke sonsu amma wallahi baruwansu da halinda mu talakawa muke ciki,kuma gaskiya zatayi halinta ko anan ko acan zamu gansu afili.
Kana mulki ruwan da talaka zaisha yagagareshi?Inna lillahi wa'inna ilaihi raji'un.
Manzon Allah S.A.W dai yagama addu'a tuni,yace:Yaa Allah duk wanda ka jibintawa wani al'amari acikin al'ummata sai yatsananta masu,yaa Allah katsananta masa wanda kuma yasauqaqa Allah kasauqaqa masa.
Nima har gobe ina akan wannan addu'a.
Allah muna qasqantar dakai gareka katausayamana,kasauqaqa mana,kakarba mana ibadunmu lallai Kai mai ikone akan haka.
0 comments:
Post a Comment