Karka yarda azuminka yaqi samun kar6uwa wajen Allah.
Hakika azumi yana daga cikin manyan ibadun Allah,shiyasa hadithi yatabbata daga manzon Allah S.A.W wanda Imamu Muslim yafitar dashi
من صام يوما في سبيل الله باعد الله بذلك اليوم وجهه النار سبعين خريفا.
Ma'ana : duk wanda ya azumci wani wuni saboda Allah,Allah zainisanta fuskarsa(zai nisantashi) daga wuta tazarar nisan shekaru 70 tsakaninshi da'ita.
Haka imamul Bukhari ya fitar da hadithi:
إذادخل رمضان فتحت أبواب الجنة،وغلقت أبواب جهنم وسلسلت الشياطين.
Ma'ana:dazarar Ramadan yashigo Allah cikin hikimarsa da ikonsa yanasa abude kofofin aljannah,ana rufe kofofin jahannama na kuma daure kangararrun shaidanu.
Mai azumi yana shiga aljannah tawata qofa tamusamman(Rayyan)
TO AMMAFA MANZON ALLAH S.A.W YA FADA CEWA:DAYAWA ANA SAMUN MAI AZUMI BAYA SAMUN KOMAI AMATSAYIN LADA/SAKAMAKON AZUMINSA ,SAI DAI KAWAI YA SHA YUNWA DA QISHIN RUWA KAWAI.Kenan yayi azumin amma Allah bashida buqatar azuminsa don haka bai kar6a ba.
WACE ASARA TAFI ACE YADDA AKE WANNAN IBADA MUHIMMIYA ACIKIN IRIN WANNAN LOKACIN DAMUKE CIKI NA TSANANIN ZAFIN RANA ,ACE BA'A KARBI AZUMIN MUTUMBA.ANYA AKWAI ASARAR DATAFI WANNAN?
DAGA CIKIN DALILAN DAKE IYASA ALLAH YAQI KARBAR AZUMIN MUTUM AKWAI:
1-Qarya,
2-Sata,
3-Giba,
4-Annamimanci,
5-Ha'inci,
6-Maganganun banza(batsa)
7-Kallon finafinan bats a
8-Qasqantarda dan uwanka musulmi,
9-Qintaimakon wanda kasan yana buqatar taimakonka,bayan kanada halin taimakon
10-Zage-zage/fara
11-Hada jiki da mace waddaba muharramarkaba/namijinda ha muharraminkiba
12-Niyyar karya azumi,
13-Yawan koke/magana akan cewa azumin akwai wahala
Dadai sauransu.
Fatanmu da ddu'armu Allah yatausaya mana yakar6a mana azuminmu dasauran ibadunmu.
0 comments:
Post a Comment