Girman kai rawanin tsiya.
To tabbas wannan abu haka yake,domin shi girman yana jawo abubuwa marasa dadi ga ma'abocinsa.Kadan daga cikin illar girman kai akwai:
-yana sa maishi yakaskantar da duk wanda bashiba
-yanasa maishi ganin girman kanshi fiyeda kowa
-yanasa kafircema ni'imar Allah
-yanasa kin karbar gaskiya ko aiki da ita
-yanasa jiji dakai
-yana haifarda gaaba
-yana haifarda hassada
-yana haifarda izgilanci ga bayin Allah akan matsayin dashi Allah ya'ajiyesu
-yanasa mutum yarasa imani
-yana jawoma maiyinsa halaka
-yana haramta maishi shiga aljannah
-yana sabbaba shiga wuta
Saboda manzon Allah S.A.W yayi bayanin abunda ake cema girman kai cikin kalmomi guda biyu:
1-Raina mutane da
2-Qin gaskiya
Duka matsayin daka samu kanka karka sake ka raina mutum,sau dayawa zakaga mutum cikin 'yan uwansa ko cikin abokai idan Allah ya daukakashi saikaga duk wanda baida matsayi irin nasa bai ishesa kalloba.saiya dunga ganin kaskancine yaje yaziyarci yar uwarshi/dan uwanshi want,cibayane yakaima abokinashi want saboda wani abuda Allah yahore masa.
Bayan mazon Allah S.A.W yace:ya ishi zama laifi agaban Allah mutum yajema Allah ya qasqantarda dan uwansa musulmi.
Allah yatsaremu da girman kai,domin shine yake hana mutum karbar gaskiya saboda yana ganin Kamar duk wanda zai fada masa gaskiya baikai matsayin dazai fada mashiba.
0 comments:
Post a Comment