Dan uwa,ko kana lura/kula da abunda yake fitowa daga bakinka?
Ko kaasan Harshenka yana'iya jefaka wuta?
Ko kasan mafiyawan gabar da tafi halakar da mutum Harshene?
قال الله في محكم تنزيله:ولا تقف ماليس لك به علم إن السمع والبصر والفؤادكل أولئك كان عنه مسئولا(سورة الإسراء ٣٦).
Ma'ana ;karka bibiyi/karkafadi abunda bakada ilimi/masaniya/tabbaci akansa,kayi bincike cikin duk abunda zaka fada,saboda jinka ,daganinka dazuciyarka duk za'a tambayeka gamedasu.
قال ابن عباس:أيلا تقل،وقال العوفي:لا ترم أحدابماليس لك به علم،وقال محمد ابن الحنفية:يعني شهادة الزور،
وقال قتادة:لاتقل:رأيت ولم تر،وسمعت،ولم تسمع،وعلمت ولم تعلم،فإن الله سائلك عن ذلك كله.
وقوله:كل أولئكأولئك ،أي:هذه الصفات من السمع والبصر والفؤاد،أي:يسأل العبد عنها يوم القيامة وتسأل عنه وعما عمل فيها
-Abdullahi Dan Abbas R.A yana fada cewa ayar tana cewa karka fadi abunda bakada tabbas.
-Aufi yana fada shima akan ma'anarayar:karka jefi wani daya daga cikin mutane da wata magana da bakada cikakken ilimi akan gaskiyar al'amari
-Muhammad ibn Hanafiya yana cewa:abunda Allah ke nufi shaidar zur(Qarya),
Shikuwa Imamu Qataada cewa yayi:karkace ka gani,alhalin baka ganiba,karkace kaji,alhalin bakajiba,karkace ka sani alhalin bakasaniba,domin lallai Allah saiya tambayeka akan haka.
Ibn Kathir yana cewa akan wa'yannan siffofi,tabbas Allah zai tambayi bawa akansu ranar alkiyama,kuma suma za'a tambayesu akan wanda aka horemasu,kuma za'a tambayesu meya'aikata dasu.
وقال تعالى:مايلفظ من قول إلا لديه رقيب عتيد(ق:١٨).
Babu wata magana dawani mai magana zai furta faace akwai mala'ika atredashi yana kiyaye dukkan abunda yake fada kuma yana rubutawa.
Hakanan Allah yaja hankalinmu acikin suratul infitar:
وإن عليكم لحافظين ١٠ كراماكاتبين ١١ يعلمون ما تفعلون ١٢
Yaa kai Dan Uwa kakula kakame harshenka daga aibata mutane musamman akan abunda bakada tabbas.
Saboda sau dayawa bawa zaiyi wata magana baya kodamuwa da maganar saboda yana hangen ai qaramar maganace amma ajefashi jahannama adalilinta.
Wata rana Abi Musa ya tambayi manzon Allah :wane musulmine yafi daraja awajen Allah,sai manzon Allah yace:shine Wanda musulmai suka kubuta daga sharrin harshensa da hannayensa.Ai baya curar da musulmai da bakinsa tahanyar yimasa:
Qarya,
Qage/QazafiQazafi,
Giba,
Annamimanci,
Da'abunda yayi kamada wيعدلها
اعلم أنه ينبغى لكل مكلف أن يحفظ لسانه عن جميع الكلام إلا كلاما فيه المصلحة،ومتى استوى الكلام وتركه فى المصلحة،فالسنة الإمساك عنه،لأنه قد ينجر الكلام المباح إلى حرام أو مكروه،والسلامة لا يعدلها شيء.
Kasani Dan uwa dole akan duk wani mukallafi yakiyaye harshensa akan furta maganganu idan ba magana bane dayan akwai maslaha cikin fadanta,kuma duk lokacinda yin magana da barin yinta sukazamo dai-dai wajen maslaha, to asunnance yin shurun shiyafi,domin sau dayawa zakaga maganar dayinta ya halatta ba laifibane amma saita jawo haramun ko abunqi.Don haka babufa abunda yakamo zaman lafiya.
Allah yakiyayemu daga sharrin harsunanmu.
0 comments:
Post a Comment