Friday, February 15, 2019

KAKIYAYI TOZARTA MUTUM,(MUSAMMAN MUSULMI)

Kanaso kagama daduniya lafiya?
Kanaso alkhairinka ya yawaita?
Kanaso rayuwarka tayi albarka?
Kanaso adunga yima addu'ar alkhairi?
Kanaso ladarka tayawaita?
Kanaso maqiyanka suqasqanta?
Kanaso adunga yima zaton alkhairi?
Kanaso jama'a susoka?
Kanaso Allah yasoka?
Tofa babu makawa saika girmama tareda mutunta mutane aduk inda kahadu dasu,musamman musulmi,musamman dan uwanka,musamman wa'yanda kasani.
Allah dakansa yabayyana mana yadda yakarrama kuma yafifita dan Adam(mutum)akan sauran halittu,cikin fadarsa:
ولقدكرمنابني ءادم وحملناهمفي البترول بمرور ربنا هم من الطيبات وفضلناهم على كثيرممن خلقناتفضيلا(الإسراء:٧٠).
Ma'ana:Tabbas mun daraja/karrama Dan Adam kuma dirashi aka tudu(was a)da'ababen hawan da'aka hore masa,dacikin teku,kuma Allah yace munkuma azurtasu da abubuwa masu dadi,sannan muka fifitasu akan mafiyawa daga cikin abubuwan damuka halitta fifitawa.(isra'i:70).
Hakanan Luqmanul Hakim cikin nasihohin dayakema dansa da'Allah yabamu labari acikin suratul Luqman,bayan yayi mashi nasiha,akan karyayi shirka,yatsaida Sallah,yayi umurni da aiki maikyau,yayi hani daga mummuna yakumayi hakuri akan jarrabawa...,sai kuma Allah face:
ولاتصعرخدك للناس ولا ومش في الأرض مرحا،إن الله لا يحب كل مختار فخور(١٨).سورة لقمان
Ma'ana:karka juyarda kumcinka/fuskarka daga mutane danufin qasqantardasu,karkayi tafiya kana taqama,lallai Allah bayason duk wani mai gairman kai mai alfahari.
أي:لا تفعل ذلك يغضبك الله،ولهذاقال:إن الله لا يحب من كل مختار فخور،أي:مختال معجب في نفسه،فخور:أي على غيره.
Ai karka aikata ha kan,Allah zaiyi fushi dakai matuqar kana wulaqanta mutane,shiyasa Allah yace bayason maitaqama ,ai mai burge Kansas(mai jijida kai),mai alfahari gawaninsa. 
 Asuratul Isra'i haryanzu Allah yana fara:ولا ومش فى الأرض مرحبا إنك لن  تخرق الأرض ولن تبلغ الجبالطولا(٣٧).
Allah yana qara jaddadawa karkayi tafiya acikin qasa kana mai alfahari da taqama,domin duk yadda kake ganin ka kai /ka'isa bazaka iya tsaga qasaba saboda girmanka hakanan bazakai girman tsaunikaba(duwatsu manya).
عن أبي هريرة رضي الله  عنه،عن النبي صل الله عليه وسلم قال:بينمارجل يمشي فيمن كان قبلكم،وعليه بردان يتبختر فيهما،إذ خسف به الأرض،فهو يتجلجل فيها إلى يوم القيامة(البخاري:٥٧٨٩).
Abi Huraira R.A yace,manzon Allah S.A.W yace:wata rana wani mutum cikin al'ummar dasukazo kafiku,yana tafiya cikin tufafi na alfarma yana taqama acikin wannan kayan yana jiji dakai,yana raina mutane,kawai sai Allah yanitsar dashi cikin qasa ma'ana qasa qasa tatsage yafada manzon Allah yace haryanzu yana ta tafiya yana qara nitsewa har ranar alkiyama.
Hakanan Imamu Muslim ya fitarda Hadithi,:
قال رسول الله صل الله عليه وسلم:إن الله أوحى إلي أن تواضعوا،حتى لا يفخر أحد على أحد،ولا يبغى أحد على أحد.
Manzon Allah yana cewa :Allah yayi Mani wahayi dacewa kuqasqantar da kai ga 'yan uwanku musulmai,harya kasance babu wani daya dayake yima wani alfahari akan yafishi mat say I ko wata ni'ima da'Allah yayi masa,kuma  babu wani daya dayake  zaluntar wani dan uwanshi musulmi. 
Hakanan Abi Huraira bada labarin hadithin dayaji daga manzon Allah S.A.W:
أن رسول  الله صل الله عليه وسلم قال:ما تواضع أحدا لله إلا رفعه الله.رواه مسلم
Manzon Allah S.A.W yace: babu wani daya dazai qaskantar dakanshi saboda Allah faace sai Allah ya daga darajarsa.
Don haka yaakai Dan uwa Kasani awani bangare na wani had it hi,manzon Allah yana cewa ya ishi mutum sharri aranar alqiyama yaje gaban Allah yawulaqanta dan uwansa musulmi,
عن أبي هريرة رضي الله عنه،قال:قال رسول الله صل الله عليه وسلم....المسلم أخو المسلم لا يظلمه،ولا يخذله،ولا يكذبه،ولا يحقره،التقوى ههنا،بحسب امرىء من الشر:أن يحقر أخاه المسلم كل المسلم على المسلم حرام:دمه،وماله،و عرضه.
رواه مسلم.
Abi Huraira R.A yace: manzon Allah S.A.W yace:musulmi Dan uwan musulmine:
-kada yazalunceshi,
-Kada yatozartashi(yaqitaimakonsa idan yana neman taimako wajensa kuma yanada iko),
-kada yaqaryatashi/yadunga qaryata musulmi dan uwansa,
-kada yarainashi,kodan yaga Allah ya fifitashi dawata ni'ima yadauka yafishi,
Tsoron Allah anan yake,sai manzon Allah S.A.W yayi nuni zuwa qirjinsa.(tsoron Allah azuciya yace,sai gabobi sutabbatar da gaskiyar hakan ko rashin gaskiyarsa),
Sai manzon Allah yace:ya'isa yazama sharri gamutum,yawulaqanta Dan  uwansa musulmi(ma'ana ko mutum yayi abunda yakamata na ibada, bashida laifin komai amma sai yajema Allah ya qasqantar tareda wulaqanta Dan uwansa musulmi,to wanna laifin ya isa yazama sharri(bala'i)dazai jawo masa azabar Allah).
Manzon Allah yacigaba dacewa awaken kowane musulmi haramunne 
-ya zubar dajininsa,
-yataba dukiyarsa (sai dayardarsa,kuma cikin dadin rai),
-yaci/yataba/yashiga cikin mutuncinsa.
Allah yataimakemu wajen mutunta junanmu dakuma ganin qimarsu,Allah yagafarta mana laifukanmu,Allah yaba yan uwanmu marasa lafiya ,lafiya.Ameen



0 comments:

Post a Comment