• This is Slide 1 Title

    This is slide 1 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

  • This is Slide 2 Title

    This is slide 2 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

  • This is Slide 3 Title

    This is slide 3 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

Saturday, July 13, 2019

GYARAKAYANKA

Dayawan Mutane basa yada sallama,musamman wanda Allah yayima falala ta dukiya,ilimi ko matsayi hardama wasu talakawan.Duk duniya babu mai matsayin Annabi S.A.W amma duk dahaka har yara qanana yanayima sallama.Anas dan malik R.A yawuce tawajen yara,sai yayi musu sallama,sai yace:manzon Allah S.A.W yakasance yana aikata haka.(BKH&MUS)
  SANNAN MULURA DAKYAU, DUK WANDAKE YIMAKA SALLAMA IDAN YA SAMEKA AWANI GURI ZAKAJI KANA SONSHI.KAMAR YADDA YAZO A HADISAN ANNABI S.A.W YACE:BAZAKU SHIGA ALJANNAH BA HAR SAI KUNYI IMANI,BAZAKUYI IMANIBA HAR SAI KUNSO JUNA,BANA SANAR DAKU WANI ABUBA WANDA IDAN KUNA AIKATASHI ZAKUSO JUNA?SAI YACE KU YADA SALLAMA ATSAKANINKU
  ANTABAYI MANZON ALLAH,IDAN  MUTANE SUKA HADU WANENE ZAI FARA YIMA WANI SALLAMA?SAI YACE:WANDA YAFI MATSAYI AWAJEN ALLAH.(Tirmizi)
Kenan duk wanda yake fara yi maka sallama idan kun hadu,akwai yiwuwar yana da matsayi wajen Allah.Yi kokari kaima kashiga cikinsu.
 Hakanan MANZON ALLAH YACE:WANDA KE SAMAN ABUN HAWA ZAIYIMA WANDA YAKE  TAFIYA  AQAFA ASALLAMA WANDA YA KE TAFIA QASA(DAQAFA) ZAIYIMA WANDA KE ZAUNE..
 (BUKH&MUS) Allah yabamu ikon koyi da manzo s.a.w wajen yada sallama.
AMEEN.

Saturday, July 6, 2019

SUNNAH KO SUNA?

Baya daga cikin karantarwar sunnar manzon Allah S.A.W,wa'yansu dabi'u wanda dayawa yara masu tasowa ko kuma ince matasan dasuke Kiran kansu ahlussunnah sukayi fice akansu.
Kuma mafi yawa sunfi aiwatar dawannan dabi'u ga wa'yanda suke bin hanyarsu.Kadan daga cikin wa'yannan dabi'u akwai:
*Tsarkake kai,
*Jiji da kai,
*Girman kai,
*Ganin fifikon kansu akan wani
*Qasqantarda mutane
*Qin girmama nagaba dasu
*Hassada.
Shifa manzon Allah baitaba koyarda almajiransa daya daga cikin wa'yannan halayenba,baikuma taba aiwatar dasuba akan mutanensaba.
Tareda kasancewarsa Wanda yafi kowa daraja da matsayi Amma,har makiya sun tabbatarda kyawawan dabi'un manzo S.A.W,kamarsu;
-Qaskantarda kai(mutunta mutane)
-Girmamasu,
-Rashin raina mutume,
-Nuna soyayya ga mutanensa,
-Sakin fuska idan ya hadu da mutum(fara'a)
-Nuna damuwa akan damuwar wani
-Riqe sirrin mutane,
-Son alkhairi ga mutane,
-Taimaka ma mutanensa,
-Cika alkawari,
-Rikon amaana,
-Kyamar ganin anci mutuncin wani,
-Baya gorantawa idan yayi alkhairi,
-Yana son cigaban dan uwansa,
-Baya ganin kyashi akan cigaba/nasarar dan uwansa(musulmi)
-Baya Qin taimakon mutum matuqar yanada abunda akazo nema.
-Baya bibiyar mutum akan saiya gano aibunsa/laifinsa,
-Yana kyauta taban mamaki
-Bashida rowa,
Wa'yannan kadanne daga cikin kyawawan halaye na manzo S.A.W da dayawanmu muke alaqanta kanmu da ma'abota bin sunnarsa(ahlussunnah)
Nidakai saimu yimakanmu adalci akan shin:
-muna koyida wa'yannan kyawawan  halayennasa?
-muna daukar mutuncin 'yan uwanmu da muhimmanci?
-muna sakin fuska idan mukaga 'yan uwannmu?
-a masallaci kadai ake koyida manzon Allah S.A.W
اللإسلامية،إحترام أهل السبق والعلم والفضل،ومذا احترام الصغير للكبير،ومعرفةأقدارالناس يتفاضلون بالإسلام،والعلم والتقوى،لابالحسب والنسب والمال.
والله الموفق.
Allah ya'azurtamu da jin tsoronsa hakikanin jin tsoronsa,wanda acikin hakanne zamu samu dukkan halaye da dabi'u irin wanda Allahn yakeso kuma yake yabon masu su.


Friday, June 28, 2019

DUK WANDA KAGA YA KAUCE HANYA BA DARIYA ZAKAYIBA

Sau dadama idan mutum yaganshi cikin masu yin abunda yakamata(masu bin dokokin Allah) sai yadauka duk wanda bashiba halakakkene.
Eh tabbas duk wanda yabijirema hanyar Allah ya halaka matuqar ya mutu akan wannan mummunar hanya.Amma kai idan kaga wani ahakaba dariya zakayi ba.
Kaima ba dabararka bane dacene daga Allah.Kuma ka himmatu afili da boye wajen son kaga yadawo hanya,ta hanyar yimasa addu'a tsakaninka da Allah agaban idonsa da bayan idonsa.
Idan kasamu dama kuma sai kajawo hankalinsa akan tsayin abunda yake aikatawa.
Domin indai yazama dabi'ar mutumne tattauna matsalar wani ta bangaren  aibatawa,ko kuma kayita bibiyar mutum saika gano laifinda yake aikatawa kawai dan aibata wannan mutum to tabbas kaima akwai yiwuwar Allah yajarabceka da wannan aikin.
Sai bincike don yanke hukunci misali ga alkali akan wani mutum,ko wani maisasanci yabinciki yadda abu yafar tsakanin mutanen da suka samu rashin jituwa Dan samun maslaha shima ba laifibane.
 Rike sirrin dan uwanka musulmi yanada matuqar mahimmanci koda yaushe mudunga kyautatama 'yan uwanmu zato.Allah yasa mudace.Ameen

Wednesday, June 26, 2019

GYARA KAYANKA

Bayaushe yana karin magana dayake cewa;
Girman kai rawanin tsiya.
To tabbas wannan abu haka yake,domin shi girman yana jawo abubuwa marasa dadi ga ma'abocinsa.Kadan daga cikin illar girman kai akwai:
-yana sa maishi yakaskantar da duk wanda bashiba
-yanasa maishi ganin girman kanshi fiyeda kowa
-yanasa kafircema ni'imar Allah
-yanasa kin karbar gaskiya ko aiki da ita
-yanasa jiji dakai
-yana haifarda gaaba
-yana haifarda hassada
-yana haifarda izgilanci ga bayin Allah akan matsayin dashi Allah ya'ajiyesu
-yanasa mutum yarasa imani
-yana jawoma maiyinsa halaka
-yana haramta maishi shiga aljannah
-yana sabbaba shiga wuta
Saboda manzon Allah S.A.W yayi bayanin abunda ake cema girman kai cikin kalmomi guda biyu:
1-Raina mutane da
2-Qin gaskiya
Duka matsayin daka samu kanka karka sake ka raina mutum,sau dayawa zakaga mutum cikin 'yan uwansa ko cikin abokai idan Allah ya daukakashi saikaga duk wanda baida matsayi irin nasa bai ishesa kalloba.saiya dunga ganin kaskancine yaje yaziyarci yar uwarshi/dan uwanshi want,cibayane yakaima abokinashi want saboda wani abuda Allah yahore masa.
Bayan mazon Allah S.A.W yace:ya ishi zama laifi agaban Allah mutum yajema Allah ya qasqantarda dan uwansa musulmi.
Allah yatsaremu da girman kai,domin shine yake hana mutum karbar gaskiya saboda yana ganin Kamar duk wanda zai fada masa gaskiya baikai matsayin dazai fada mashiba. 

Monday, May 20, 2019

ALAQAR MUSULMI DA RAMADAN 2

Karka yarda azuminka yaqi samun kar6uwa wajen Allah.
Hakika azumi yana daga cikin manyan ibadun Allah,shiyasa hadithi yatabbata daga manzon Allah S.A.W wanda Imamu Muslim yafitar dashi
من صام يوما في سبيل الله باعد الله بذلك اليوم وجهه النار سبعين خريفا.
Ma'ana : duk wanda ya azumci wani wuni saboda Allah,Allah zainisanta fuskarsa(zai nisantashi) daga wuta tazarar nisan shekaru 70 tsakaninshi da'ita.
Haka imamul Bukhari ya fitar da hadithi:
إذادخل رمضان فتحت أبواب الجنة،وغلقت أبواب جهنم وسلسلت الشياطين.
Ma'ana:dazarar Ramadan yashigo Allah cikin hikimarsa da ikonsa yanasa abude kofofin aljannah,ana rufe kofofin jahannama na kuma daure kangararrun shaidanu.
Mai azumi yana shiga aljannah tawata qofa tamusamman(Rayyan)
TO AMMAFA MANZON ALLAH S.A.W YA FADA CEWA:DAYAWA ANA SAMUN MAI AZUMI BAYA SAMUN KOMAI AMATSAYIN LADA/SAKAMAKON AZUMINSA ,SAI DAI KAWAI YA SHA YUNWA DA QISHIN RUWA KAWAI.Kenan yayi azumin amma Allah bashida buqatar azuminsa don haka bai kar6a ba.
WACE ASARA TAFI ACE YADDA AKE WANNAN IBADA MUHIMMIYA ACIKIN IRIN WANNAN LOKACIN DAMUKE CIKI NA TSANANIN ZAFIN RANA ,ACE BA'A KARBI AZUMIN MUTUMBA.ANYA AKWAI ASARAR DATAFI WANNAN?
DAGA CIKIN DALILAN DAKE IYASA ALLAH YAQI KARBAR AZUMIN MUTUM AKWAI:
1-Qarya,
2-Sata,
3-Giba,
4-Annamimanci,
5-Ha'inci,
6-Maganganun banza(batsa)
7-Kallon finafinan bats a
8-Qasqantarda dan uwanka musulmi,
9-Qintaimakon wanda kasan yana buqatar taimakonka,bayan kanada halin taimakon
10-Zage-zage/fara
11-Hada jiki da mace waddaba muharramarkaba/namijinda ha muharraminkiba
12-Niyyar karya azumi,
13-Yawan koke/magana akan cewa azumin akwai wahala
Dadai sauransu.
Fatanmu da ddu'armu Allah yatausaya mana yakar6a mana azuminmu dasauran ibadunmu.

Wednesday, May 15, 2019

ANYA KUWA DIMOKRADIYYA AKE?

صدق رسول الله صل الله عليه وسل إذقال:أخوف ما أخف على أمتي الأئمة المضلون.

Tabbas manzon Allah yayi gaskiya ,domin yafada cewa:abunda nafijima al' ummata tsoronsa shine jagorori batacci/batattu.

Abunda nalura dashi a Nigeria:
*Musulmi bashida 'yancin magana
*Jami'an tsaro na DSS sun kware wajen kama malaman addinin musulunci
*Ba'ason malamin addini yakasance yana fadin gaskiya ,sai dai rufa-rufa
*Amfison malaman da suke yaqar 'yan uwansu saboda wata jam'iyyar da 80 % zuwa 90% 'yan jam'iyyar da'ake iqirarin bata masu gaskiya bace
*Anfison ana kashe 'yan uwanka kace gyara ake
*Anfi taimakon addininda ba musulunciba
*akullum ba'aso Dan kasa yasan inda ake ha'intarshi
*Jami'an tsaro sunzama karnukan farautar masu mulki
*aduk lokacinda kaji ance ankama wani saboda maganar dayayi domin tana iya jawo rikici, to zakaga musulmine
*Manyan malamai dayawa daga cikinsu sunkoma neman gamsarda masu mulki saboda maslaharsu kadai
Iyakar sanina babu malamin sunnah dayake zuga mutane suyi ta'addanci.
Duk abunda malami zai fada kodai yayi gaskiya kokuma yafadi akasin haka.Sai aduba maganarsa idan gaskiya yafada sai adauki maganarsa domin ayi gyara,idan kuma ba gaskiya bane sai warware maganarsa da hujjoji masu gamsarwa.
Mu abunda muke cewa wa'yannan abubuwan dake faruwa na kashe-kashe rayukan al'umma batareda laifin komaiba sai dan suna musulmai,da agwamnatin bayane wa'yanda suke hana afadi zahirin abunda yake faruwa sunefa suke kuka suna tir da Allah wadai da abunda yake faruwa.
Sai yanzu kuma sai ace abunda yake faruwa baza'ayi maganaba.
Kai mukam mungaji da gafara sa bamuga Qahoba.
Allah Muna tawassuli da ibadar azumi damukeyi,karatul al'qur'ani dasuran ibadu Kaku6utarda bayinka da'aka tsare abisa zalunci,Allah katsare yan uwa musulmi aduk inda duke.Allah kagyara mana shuwagabanninmu.Idan kuma ba masu shir yuwa bane kadaukar mana matakin daya dace akansu.AMEEN


Friday, May 10, 2019

GASKIYA MAI DACI

Azahirin gaskiya akwai matsalolin da alokacin baya basu tsananta kamar yadda ake shan wahala yanzuba
Farkodai yakamata dukkanmu musani cewa tabbas komai yana kasancewane bisa qaddarawar Allah.Idan Allah yaso faruwar abu yana kasancewa kamar yadda yaso batareda gudummuwar kowaba.
Amma hakan baya nuni dacewa duk abunda shuwagabanni sukayi nakuskure sai ace ai haka Allah yaso babu mai iya kawo sauqi sai Allah.Abbas hakane amma;
 menene hikimar hukunta shugabanci?ko shakka babu don maslahar al'ummane.Kai shugaba dole kasani cewa talakawa nada haqqi dayawa akanka,na daga cikin haqqokin:
*tsare masu lafiyarsu,
*Tsare masu dukiyoyinsu,
*tsare masu addininsu,
*Samar da walwala acikinsu,
*Samar masu abunda yake buqtuwane na doke,
Kamar samarda ruwansha,wutan lantarki,samarda magunguna da kulada asibitocin.
Amma kash!!! Al'amarin yanada bantsoro.Azumi al'ummar musulmai sukeyi amma ruwan jarka da'ake saye yayi wahala,da kudinka kan a so kasaya babu ruwan.
Yanzu haka danike rubutunnan munyi awa saba'in da biyu(72 hours)babu wutan lantarki,adai dai lokacin da shuwagabanni basusan da matsalar wuta ko ruwa ba.Tabbas shugabanci ba abu bane mai sauqi,ammafa su sukanema kuma wallahi dukkansu dadin mulkinnan sukeji,abunda yadami talakawa su ba matsalarsubace.
Wannan wani irin canjine?
Anya kuwa masu kare shuwaganni acikin kuskure idan sunyi zasu'iya fuskantar Allah domin bada kariya akan quncin rayuwa da talaka yashiga adalilin sakaci ko nuna halin ko'inkula da shuwagabanni suke nunawa?
Koda yake nidai nagama nazari akan shuwagabanninmu,akwai wanda mune ke sonsu amma wallahi baruwansu da halinda mu talakawa muke ciki,kuma gaskiya zatayi halinta ko anan ko acan zamu gansu afili.
Kana mulki ruwan da talaka zaisha yagagareshi?Inna lillahi wa'inna ilaihi raji'un.
Manzon Allah S.A.W dai yagama addu'a tuni,yace:Yaa Allah duk wanda ka jibintawa wani al'amari acikin al'ummata sai yatsananta masu,yaa Allah katsananta masa wanda kuma yasauqaqa Allah kasauqaqa masa.
Nima har gobe ina akan wannan addu'a.
Allah muna qasqantar dakai gareka katausayamana,kasauqaqa mana,kakarba mana ibadunmu lallai Kai mai ikone akan haka.