Saturday, July 6, 2019

SUNNAH KO SUNA?

Baya daga cikin karantarwar sunnar manzon Allah S.A.W,wa'yansu dabi'u wanda dayawa yara masu tasowa ko kuma ince matasan dasuke Kiran kansu ahlussunnah sukayi fice akansu.
Kuma mafi yawa sunfi aiwatar dawannan dabi'u ga wa'yanda suke bin hanyarsu.Kadan daga cikin wa'yannan dabi'u akwai:
*Tsarkake kai,
*Jiji da kai,
*Girman kai,
*Ganin fifikon kansu akan wani
*Qasqantarda mutane
*Qin girmama nagaba dasu
*Hassada.
Shifa manzon Allah baitaba koyarda almajiransa daya daga cikin wa'yannan halayenba,baikuma taba aiwatar dasuba akan mutanensaba.
Tareda kasancewarsa Wanda yafi kowa daraja da matsayi Amma,har makiya sun tabbatarda kyawawan dabi'un manzo S.A.W,kamarsu;
-Qaskantarda kai(mutunta mutane)
-Girmamasu,
-Rashin raina mutume,
-Nuna soyayya ga mutanensa,
-Sakin fuska idan ya hadu da mutum(fara'a)
-Nuna damuwa akan damuwar wani
-Riqe sirrin mutane,
-Son alkhairi ga mutane,
-Taimaka ma mutanensa,
-Cika alkawari,
-Rikon amaana,
-Kyamar ganin anci mutuncin wani,
-Baya gorantawa idan yayi alkhairi,
-Yana son cigaban dan uwansa,
-Baya ganin kyashi akan cigaba/nasarar dan uwansa(musulmi)
-Baya Qin taimakon mutum matuqar yanada abunda akazo nema.
-Baya bibiyar mutum akan saiya gano aibunsa/laifinsa,
-Yana kyauta taban mamaki
-Bashida rowa,
Wa'yannan kadanne daga cikin kyawawan halaye na manzo S.A.W da dayawanmu muke alaqanta kanmu da ma'abota bin sunnarsa(ahlussunnah)
Nidakai saimu yimakanmu adalci akan shin:
-muna koyida wa'yannan kyawawan  halayennasa?
-muna daukar mutuncin 'yan uwanmu da muhimmanci?
-muna sakin fuska idan mukaga 'yan uwannmu?
-a masallaci kadai ake koyida manzon Allah S.A.W
اللإسلامية،إحترام أهل السبق والعلم والفضل،ومذا احترام الصغير للكبير،ومعرفةأقدارالناس يتفاضلون بالإسلام،والعلم والتقوى،لابالحسب والنسب والمال.
والله الموفق.
Allah ya'azurtamu da jin tsoronsa hakikanin jin tsoronsa,wanda acikin hakanne zamu samu dukkan halaye da dabi'u irin wanda Allahn yakeso kuma yake yabon masu su.


0 comments:

Post a Comment