Saturday, July 13, 2019

GYARAKAYANKA

Dayawan Mutane basa yada sallama,musamman wanda Allah yayima falala ta dukiya,ilimi ko matsayi hardama wasu talakawan.Duk duniya babu mai matsayin Annabi S.A.W amma duk dahaka har yara qanana yanayima sallama.Anas dan malik R.A yawuce tawajen yara,sai yayi musu sallama,sai yace:manzon Allah S.A.W yakasance yana aikata haka.(BKH&MUS)
  SANNAN MULURA DAKYAU, DUK WANDAKE YIMAKA SALLAMA IDAN YA SAMEKA AWANI GURI ZAKAJI KANA SONSHI.KAMAR YADDA YAZO A HADISAN ANNABI S.A.W YACE:BAZAKU SHIGA ALJANNAH BA HAR SAI KUNYI IMANI,BAZAKUYI IMANIBA HAR SAI KUNSO JUNA,BANA SANAR DAKU WANI ABUBA WANDA IDAN KUNA AIKATASHI ZAKUSO JUNA?SAI YACE KU YADA SALLAMA ATSAKANINKU
  ANTABAYI MANZON ALLAH,IDAN  MUTANE SUKA HADU WANENE ZAI FARA YIMA WANI SALLAMA?SAI YACE:WANDA YAFI MATSAYI AWAJEN ALLAH.(Tirmizi)
Kenan duk wanda yake fara yi maka sallama idan kun hadu,akwai yiwuwar yana da matsayi wajen Allah.Yi kokari kaima kashiga cikinsu.
 Hakanan MANZON ALLAH YACE:WANDA KE SAMAN ABUN HAWA ZAIYIMA WANDA YAKE  TAFIYA  AQAFA ASALLAMA WANDA YA KE TAFIA QASA(DAQAFA) ZAIYIMA WANDA KE ZAUNE..
 (BUKH&MUS) Allah yabamu ikon koyi da manzo s.a.w wajen yada sallama.
AMEEN.

0 comments:

Post a Comment