Tuesday, March 5, 2019

RAYUWA DARASINE/CE(SAMU DARASHI DUK DAGA ALLAH NE)

Darussan rayuwa sunadayawa,wani darasin yana dasauki,cikin sauqi sai kadaukeshi,wani darasin kuma akwai wahala kuma yanada wahalar dauka.Sai dai abunda yakamata idan wani yana baka labarin darasinshi to karka qaryatashi karkuma kakusheshi,yikokari kafahimci darasinshi domin maiyiwuwa za'ayima jarabawa akan irin darasinshi.
 Duk wanda zai iya tattauna darasinshi narayuwa dakai to tabbas ya yarda dakai kuma ya amince dakai domin sau dayawa darussan rayuwa suna dauke da sirrin mutum,kuma babu wanda zai bayyana sirrinshi gawanda bayaso.
   Abubuwa dadama sukansa mutum ya tunkareka da darasinshi narayuwa/sirrinshi na rayuwa,kadan daga cikinsu akwai:
1-Soyayya,
2-Qauna,
3-Yarda,
4-Zaton alkhairi,
5-Aminci,
6-Abota,
7-'Yan uwantaka tajini/addini
8-Maqotaka,
9-Fahimtarka wajen son taimako,
10-Damuwarka/kulawarka da jama'a
Idan kuwa hakane to duk wanda yazomaka dawani al'amari akan darasinshi na rayuwa,to cikin abubuwa guda biyar(5)dole asamu daya(1):
-Ko dai yazamo Dan uwanka
-Ko yazama abokinka,
-Ko yazama maqocinka,
-Ko kuma yazama qasanka yake,
-Ko kuma dalibinka.
Duk cikin wa'yannan babu wanda baicancanci kulawarkaba,gwargwadon halinda kake dashi.sannan wajen saurarensa yanada kyau kayimasa kyakkyawan fahimta.Akwai inda'yar shawara kadan yake bukata daga wajenka amma idan kajuya masa baya sai yakasa kaiwa ga inda yakeson kaiwa.Akwai kuma wanda alfarmar dayake nema wajenka idan kayi mashi babu abunda zaka ragu dashi amma sai shaidan yayi tasiri acikin zuciyarka yahanaka sanya farin ciki acikin zuciyar bayin Allah,wanda adalilin taimakama wani wajen yayewar damuwarsa/bakin cikinsa kaima Allah zai yaye maka damuwa/bakin cikin ranar alkiyama,kamar yadda manzon Allah S.A.W yafadi haka acikin ingantaccen hadithi.To shikuma shaidan yana bakin cikin mumini yasmu farinciki ranar qiyama.
Abun farko dayakamata kasa aranka duk lokacin dawani yazo da wani darasinshi na rayuwa,KAYI QOQARI KA QADDARA ACIKIN ZUCIYARKA CEWA DA KAINE KAKE CIKIN DAMUWAR DAYAKE CIKI KUMA BAKA DA HANYAR DAKAKE HANGEN YAYEWARTA AKUSA YA ZAKAJI.
KO KUMA DA KAINE KAKE NEMAN SHAWARA AKAN IRIN DAMUWAR DAYAKE CIKINTA KUMA YAKE NEMAN SHAWARAR DAZAI SAMU MAFITA,YA ZAKAYI?
Ataqaice duk lokacin dawani yazo maka dadamuwarsa/neman shawararka akan halin dayake ciki,to kajigina damuwarshi dakanka, idan Kaine awannan halin yaya zakaji.
Sau dayawa muna da dabi'ar idan dan uwanmu yazo mana dawata buqata/damuwa sai mununa masa kamar rashin imanine /rashin hakuri,a'a ba haka al'amarin yakeba,Abi Huraira R.A ya ruwaito hadithi wanda Imam Muslim yafitar dash:
عن أبي هريرة رضي الله عنه قال:خرج رسول الله صل الله عليه وسلم ذات يوم  فإذاهو بأبى بكر و عمر-رضى الله عنهما-فقال:ما أخرجكما من بيوتكما هذه الساعة؟.قالا:الجوع يا رسول الله.قال:وأنا،والذى نفسي بيده،لأخرجنى الذى أخرجكما.قوما !فقاما معه،،فأتى رجلا من الأنصار.....الى أخ
Daga Abi Huraira R.A yace:manzon Allah S.A.W yafita wata rana,sai ga Abubakar da Umar R.A.M,sai manzon Allah yatambayesu meyafito daku daga gidajenku a irin wannan lokacin?.Sai sukace:Yunwa tafito damu ya manzon Allah.Sai yace:nima,na rantseda wanda raina ke hannunsa,abunda yafito daku shiyafito dani daga gida(yunwa).Sai manzon Allah S.A.W yace: kutashi mutafi,sai sukatashi taredashi suka nufi gidan wani ansar,mutumin madina(Abu Haitham ibn Attayyihan R.A)....
Abun lura yadda manzon Allah yunwa tafito dashi daga gida tareda sauran Abokansa kuma Khalifofinsa ,nantake manzon Allah yace sutafi gidan wannan Sahabi don susamu abunda zasuci,kuma dasukaje yayi masu liyafa,har dabba yayanka masu,sukaci sukasha suka godema Allah.Dan haka duk wanda Allah ya hadaka dashi tofa yanada wani hakki akanka kaima kanada hakki akansa.
Yi kokari kazama kamar wannan sahabi mai girma dayaciyar da fiyayyen halitta S.A.W da abokansa su biyu,wajen sharema Dan uwanka kukansa.Allah yaqara mana son juna,da son taimakon juna.Allah yagafarta mana laifukanmu.

1 comments:

  1. Allah yasakada alheri,yabamu ikon taimakon junanmu,Amin

    ReplyDelete