• This is Slide 1 Title

    This is slide 1 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

  • This is Slide 2 Title

    This is slide 2 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

  • This is Slide 3 Title

    This is slide 3 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

Monday, May 20, 2019

ALAQAR MUSULMI DA RAMADAN 2

Karka yarda azuminka yaqi samun kar6uwa wajen Allah.
Hakika azumi yana daga cikin manyan ibadun Allah,shiyasa hadithi yatabbata daga manzon Allah S.A.W wanda Imamu Muslim yafitar dashi
من صام يوما في سبيل الله باعد الله بذلك اليوم وجهه النار سبعين خريفا.
Ma'ana : duk wanda ya azumci wani wuni saboda Allah,Allah zainisanta fuskarsa(zai nisantashi) daga wuta tazarar nisan shekaru 70 tsakaninshi da'ita.
Haka imamul Bukhari ya fitar da hadithi:
إذادخل رمضان فتحت أبواب الجنة،وغلقت أبواب جهنم وسلسلت الشياطين.
Ma'ana:dazarar Ramadan yashigo Allah cikin hikimarsa da ikonsa yanasa abude kofofin aljannah,ana rufe kofofin jahannama na kuma daure kangararrun shaidanu.
Mai azumi yana shiga aljannah tawata qofa tamusamman(Rayyan)
TO AMMAFA MANZON ALLAH S.A.W YA FADA CEWA:DAYAWA ANA SAMUN MAI AZUMI BAYA SAMUN KOMAI AMATSAYIN LADA/SAKAMAKON AZUMINSA ,SAI DAI KAWAI YA SHA YUNWA DA QISHIN RUWA KAWAI.Kenan yayi azumin amma Allah bashida buqatar azuminsa don haka bai kar6a ba.
WACE ASARA TAFI ACE YADDA AKE WANNAN IBADA MUHIMMIYA ACIKIN IRIN WANNAN LOKACIN DAMUKE CIKI NA TSANANIN ZAFIN RANA ,ACE BA'A KARBI AZUMIN MUTUMBA.ANYA AKWAI ASARAR DATAFI WANNAN?
DAGA CIKIN DALILAN DAKE IYASA ALLAH YAQI KARBAR AZUMIN MUTUM AKWAI:
1-Qarya,
2-Sata,
3-Giba,
4-Annamimanci,
5-Ha'inci,
6-Maganganun banza(batsa)
7-Kallon finafinan bats a
8-Qasqantarda dan uwanka musulmi,
9-Qintaimakon wanda kasan yana buqatar taimakonka,bayan kanada halin taimakon
10-Zage-zage/fara
11-Hada jiki da mace waddaba muharramarkaba/namijinda ha muharraminkiba
12-Niyyar karya azumi,
13-Yawan koke/magana akan cewa azumin akwai wahala
Dadai sauransu.
Fatanmu da ddu'armu Allah yatausaya mana yakar6a mana azuminmu dasauran ibadunmu.

Wednesday, May 15, 2019

ANYA KUWA DIMOKRADIYYA AKE?

صدق رسول الله صل الله عليه وسل إذقال:أخوف ما أخف على أمتي الأئمة المضلون.

Tabbas manzon Allah yayi gaskiya ,domin yafada cewa:abunda nafijima al' ummata tsoronsa shine jagorori batacci/batattu.

Abunda nalura dashi a Nigeria:
*Musulmi bashida 'yancin magana
*Jami'an tsaro na DSS sun kware wajen kama malaman addinin musulunci
*Ba'ason malamin addini yakasance yana fadin gaskiya ,sai dai rufa-rufa
*Amfison malaman da suke yaqar 'yan uwansu saboda wata jam'iyyar da 80 % zuwa 90% 'yan jam'iyyar da'ake iqirarin bata masu gaskiya bace
*Anfison ana kashe 'yan uwanka kace gyara ake
*Anfi taimakon addininda ba musulunciba
*akullum ba'aso Dan kasa yasan inda ake ha'intarshi
*Jami'an tsaro sunzama karnukan farautar masu mulki
*aduk lokacinda kaji ance ankama wani saboda maganar dayayi domin tana iya jawo rikici, to zakaga musulmine
*Manyan malamai dayawa daga cikinsu sunkoma neman gamsarda masu mulki saboda maslaharsu kadai
Iyakar sanina babu malamin sunnah dayake zuga mutane suyi ta'addanci.
Duk abunda malami zai fada kodai yayi gaskiya kokuma yafadi akasin haka.Sai aduba maganarsa idan gaskiya yafada sai adauki maganarsa domin ayi gyara,idan kuma ba gaskiya bane sai warware maganarsa da hujjoji masu gamsarwa.
Mu abunda muke cewa wa'yannan abubuwan dake faruwa na kashe-kashe rayukan al'umma batareda laifin komaiba sai dan suna musulmai,da agwamnatin bayane wa'yanda suke hana afadi zahirin abunda yake faruwa sunefa suke kuka suna tir da Allah wadai da abunda yake faruwa.
Sai yanzu kuma sai ace abunda yake faruwa baza'ayi maganaba.
Kai mukam mungaji da gafara sa bamuga Qahoba.
Allah Muna tawassuli da ibadar azumi damukeyi,karatul al'qur'ani dasuran ibadu Kaku6utarda bayinka da'aka tsare abisa zalunci,Allah katsare yan uwa musulmi aduk inda duke.Allah kagyara mana shuwagabanninmu.Idan kuma ba masu shir yuwa bane kadaukar mana matakin daya dace akansu.AMEEN


Friday, May 10, 2019

GASKIYA MAI DACI

Azahirin gaskiya akwai matsalolin da alokacin baya basu tsananta kamar yadda ake shan wahala yanzuba
Farkodai yakamata dukkanmu musani cewa tabbas komai yana kasancewane bisa qaddarawar Allah.Idan Allah yaso faruwar abu yana kasancewa kamar yadda yaso batareda gudummuwar kowaba.
Amma hakan baya nuni dacewa duk abunda shuwagabanni sukayi nakuskure sai ace ai haka Allah yaso babu mai iya kawo sauqi sai Allah.Abbas hakane amma;
 menene hikimar hukunta shugabanci?ko shakka babu don maslahar al'ummane.Kai shugaba dole kasani cewa talakawa nada haqqi dayawa akanka,na daga cikin haqqokin:
*tsare masu lafiyarsu,
*Tsare masu dukiyoyinsu,
*tsare masu addininsu,
*Samar da walwala acikinsu,
*Samar masu abunda yake buqtuwane na doke,
Kamar samarda ruwansha,wutan lantarki,samarda magunguna da kulada asibitocin.
Amma kash!!! Al'amarin yanada bantsoro.Azumi al'ummar musulmai sukeyi amma ruwan jarka da'ake saye yayi wahala,da kudinka kan a so kasaya babu ruwan.
Yanzu haka danike rubutunnan munyi awa saba'in da biyu(72 hours)babu wutan lantarki,adai dai lokacin da shuwagabanni basusan da matsalar wuta ko ruwa ba.Tabbas shugabanci ba abu bane mai sauqi,ammafa su sukanema kuma wallahi dukkansu dadin mulkinnan sukeji,abunda yadami talakawa su ba matsalarsubace.
Wannan wani irin canjine?
Anya kuwa masu kare shuwaganni acikin kuskure idan sunyi zasu'iya fuskantar Allah domin bada kariya akan quncin rayuwa da talaka yashiga adalilin sakaci ko nuna halin ko'inkula da shuwagabanni suke nunawa?
Koda yake nidai nagama nazari akan shuwagabanninmu,akwai wanda mune ke sonsu amma wallahi baruwansu da halinda mu talakawa muke ciki,kuma gaskiya zatayi halinta ko anan ko acan zamu gansu afili.
Kana mulki ruwan da talaka zaisha yagagareshi?Inna lillahi wa'inna ilaihi raji'un.
Manzon Allah S.A.W dai yagama addu'a tuni,yace:Yaa Allah duk wanda ka jibintawa wani al'amari acikin al'ummata sai yatsananta masu,yaa Allah katsananta masa wanda kuma yasauqaqa Allah kasauqaqa masa.
Nima har gobe ina akan wannan addu'a.
Allah muna qasqantar dakai gareka katausayamana,kasauqaqa mana,kakarba mana ibadunmu lallai Kai mai ikone akan haka.



Wednesday, May 8, 2019

ALAQAR MUSULMI DA RAMADANA

Ko shakka babu yakamata aga canji arayuwar musulmi acikin ramadana.
Shidai watan Ramadan watane mai falalar gaske domin lokacine da Allah yake yima bayinsa rahma,gafara tareda 'yantasu daga wuta zuwa aljannah.Anaso musulmi lokacin ramadana yakasance mai:
Hakuri
Tausayi
Karamci
Yafiya
Kyauta
Yawan ibada
Karatun alqur'ani
Kame harshensa daga Qarya
Rintse ganinsa
Kiyaye jinsa
Kyautatama iyaye
kyautatama Moqota
kyautatama abokansa
Rufama dan uwansa asiri
Girmama Dan uwansa musulmi
Mai amfanar da jama'a
Sai mutambayi kanmu haka muke?
Saboda mu'amalarmu dayawa tananuna rashin tasirantawa da ramadana,mun dauka azumi shine kawai barin ci dasha da jima'i.
*sai kaga mutum yana azumi amma qarya itace sana'arsa,bayan manzon Allah S.A.W acikin hadithi ingantacce yace:duk wanda bai bar fadar qarya da aiki da itaba to fa Allah bashida buqatar barin cinsa da shansa.
*sai kaga bamu tausayama junanmu,musammam 'yan kasuwanmu sun maida lokacin Ramadan lokaci mafi tsadan kayan masarufi tareda cewa ba kayan bane ke qara tsada.
Sau dayawa saikaga anboya kayan dan asayar da tsada,har qanqara ta ruwa sai kaga ana sayenta Naira 40 #50.
To lallai ya kamata musani manzon Allah S.A.W yayi magana akan matsayin tausayi da kuma sauqaqawa  ga al'umma.
عن عائشة رضي الله عنها قالت:قال رسول الله صل الله عليه وسلم:إن الله رفيق يحب الرفق فى الأمر كله.
Daga Aisha R.A tace:Manzon Allah S.A.W ya ce: Lallai Allah mai tausayine yana son tausayi cikin al'amura gaba daya.Bukhari da Muslim suka fitar da hadithin.
و قال أنس رضي الله عنه،عن النبي صل الله عليه وسلم قال:يسرو ولا تعسرو،وبشرو ولا تنفروا.
Anas R.A yace manzon Allah S.A.W yace kusauqaqa karku tsananta ,kuma kuyi mutane bushara da abu maikyau karku koresu.
وقال صل الله عليه وسلم من يحرم الرفق يحرم الخير كله.رواه مسلم.
Hakanan manzon Allah S.A.W yace duk wanda bashida tausayi ya rasa alkhairi gaba daya.
To mike tunaninmu a irin rayuwar damuke ciki yanzu.Sai kaga wa'yanda ba muba sunfimu son junansu datausayin junansu.amma sai kaga musulmi baya son musulmi Dan uwansa yasamu sauqin rayuwa,koda yanada dalilin dazai taimakeshi bazaiyiba idanma yaga wata hanya da musulmi Dan uwansa zaisamu sauqin rayuwa zai iya hanawa.
Rayuwar damusulmai sukeyi ta wahala da anatausayin juna da ba hakaba da ansamu sauqi,saboda duk wanda kake taredasu kasan Wanda kafi kuma kasan wanda yake buqatar taimako.
Yana daga cikin hikimar farlanta azumi don mawadaci ya dandani irin abunda talaka yakeji dalilin zama da yunwa.Sai wannan yasa masa tausayi dajinqan mai qaramin karfi dayake qasa dashi.
Allah yatausaya mana yakarba mana azuminmu dasauran ibadunmu.Allah yasa mana tausayi dajinqan juna acikin zukatanmu.


Wednesday, May 1, 2019

ILLOLIN ZUWAN MATA WAJEN 'YAN TSIBBU/BOKAYE

Ana samun mata masu yawa da dabi'ar bin 'yan tsibbu da Bokaye saboda manufofi daban daban.
Amma mafi yawa abun dayake kai mata wajen bokaye dalilaine kamar haka:
*jayayyada umurnin Allah
*fada da qaddarar Allah
*sa6ama umurnin manzon Allah
*rashin imani
*rashin tausayi
*hassada
*rashin tawakkali 
Mafi yawan sihirin da mata sukafiyi shine
السحر التفريق:للتفريق بين:
الرجل وأمه
الرجل و أبيه
الرجل وأخيه
الرجل وصديقه
الرجل وشريكه في التجارة
أو التفريق بين الرجل وزوجته،و هذا النوع أخطرها و أكثرها انتشارا
Sihiruttafriq anayin sane don raba:
-Tsakanin mutum da mahaifiyarsa
-Mutum da mahaifinsa
-Mutum da Dan uwansa najini
-Mutum da abokinsa
-Mutum da abokin kasuwancinsa
-Kuma anayi dan raba tsakanin mutum da matarsa,kuma wannan au'in shiyafi hatsari kuma shiyafi yaduwa/shi mata sukafi yawanyi
Babban dalilin mata na fadawa cikin wannan halakar shine KISHI.
Akasarin mata akan kishiya suke halaka.
Wani lokacin uwargidance zakasamu dawannan matsalar,wani lokacin kuma wadda aka auro daga baya itaceke lalata gida.
Mutum yana zauneda matarsa lafiya lokaci daya saikaga yatsaneta,ko sunanta bayaso yaji an ambata,kuma daza'a tambayeshi dalilin dayasa baya sonta shikanshi baisaniba.Duk wace mai wannan mummunar dabi'ar tana  jefa kanta cikin bala'i kala-kala,daga ciki:
*Manzon Allah yace baya tareda ita;
من جنب على امرئ زوجته فليس منا.
أخرجه أبوداود
Manzon Allah S.A.W yace duk wanda yanisanta/yaraba mutum da matarsa to bataya tare damu.
*Allah tana fushi da'ita.
*ba'a karbar sallarta.
*Allah yatsinemata domin ta raba zumunci
*Tanasa mijinta yaqiyin adalci atsakanin matansa,Wanda hakan matsalane agareshi da'ita,
*tana shiga cikin masu annamimanci dukda sihirin datakeyi bai isheta kullum tana yawon hada wannan matarda mijinta,mutanenda taga suna shiri da'ita,yara da babansu wa'yanda ba 'ya'yantaba,
*tana shiga cikin masuyin giba,
*mafi yawa zaka'iske fasiqace saboda mafiyawan 'yan tsibbu da bokayen datakebi sai sunyi lalata da'ita sannan sukeyi mata aikin da take so,
*kodayaushe tana fama da ciwon zuciya saboda ciwon hassada.
*batajin kunyar zagin mutum amma agaban idonsa akasin haka.
*batajin kunyar yin qarya
*koda yaushe baka rabata da laya,ajikin skirt din ta,hannun zanenta,jikin pant din ta,cikin pillow na Maigida dasauran gurare
*komin dadewa wata rana saita baki tausayi saboda duk tsawon lokacinda akadauka tana cutama mijin da matansa lokaci daya abun zai lalace.
*duk gidahen bokaye da 'yan tsibbun datake zuwa batareda izinin maigidanta take zuwaba,mala'iku na tsine mata.
Allah ya shiryi masu wannan muguwar halayyar.