Wednesday, April 17, 2019

مفاتيح النار للنساء(MABUDAN WUTA GA MATA)

Ya ke 'yar uwa na tabbata
ke musulmace kuma kinyarda da manzon Allah S.A.W,kuma kitabbata cewa duk abunda yafada gaskiyane,to hakika Hadithi ya tabbata daga manzon Allah S.A.W:
Abdullahi Dan Abbas R.A yace:Manzon Allah S.A.W yace :annuna mani aljannah sainaga mafi yawan 'yan cikinta talakawane,kuma annuna mani wuta sainaga mafiya yawan 'yan cikinta Matane.
Haka ma Abi Hurairah da Abdullahi Dan Umar R.A sunfadi irin abunda Dan Abbas yafada suma sunjine daga bakin manzon tsira S.A.W.
 *Ko kinsani 'yar uwa daga cikin abunda yake kai mata wuta akwai;SIHIRI
السحر من مفاتيح النار للنساء،سواء كان القيام بعمل السحر أو الذهاب إلى الساحر وتصديقه.
Sihiri yana daga cikin mabudin shiga wuta ga mata,kodai takasance ita keyinsa da kanta kokuma zuwa takeyi anayi mata to duk dayane.
 Manzon Allah S.A.W yace :duk Wanda yaje yaje wajen mai sihiri yakuma yarda da abunda yafada masa,to ya kafircewa abunda aka saukarwa Muhammad S.A.W.,Dan haka babu makawa maiyin sihiri ko wanda yake zuwa ayi masa yana kafirta.
Shikuwa idan mutum yamutu kafiri babushi babu shiga aljannah.
 Sau dayawa Mata idonsu yana rufewa akan al'amarin kishiya(abokiyar zamanta)saikaga tashiga bin malaman tsibbu(bokaye)duk wani lungu dasaqo idan taji labarin irin wa'yannan batattun saitaje,saboda buqatunta,kadan daga cikin abundance take buqata ayimata sune:
*Zata buqaci asawa mijin qin abokiyar zamanta,
*Zata buqaci amaido hankalinshi kanta kadai,
*yakasance maganarta kawai yake saurare,
*Komin muhimmacin abu idan ba ita tace ayiba to bazaiyiba,
*Tana raba zumuncin miji da 'yan uwansa,
*Tanasa miji yatsani 'yayan daba nataba,
*Dukiyarsa gaba daya tana komawa karkashin ikonta
*Tana fitarda abokiyar zamanta daga cikin gidan.
 wannan kadan kenan daga cikin mugun aikin mata masu bin malaman tsibbu.
Tabbas kyautatawar mace ga mijinta yanasa mijin yaso matar,amma ba irin son dayawuce dabi'a ba.
Saboda sona Allah baya sanya mutum ya dinga bin umurnin matarsa harya sa6awa Allah.Sona Allah bayasa miji yabi ra'ayin matarsa wajen yanke zumunci tsakaninsa da 'yan uwansa,amma agefe daya kuma saikaga shi mijin yana rawar jiki wajen kyautatawa danginta.
Kuma duk laifin daxatayi bazai ta6a ganinsa amatsayin laifiba.
Shiyasa Manzon Allah S.A.W yace
عن ابن مسعود رضي الله عنه قال:سمعت رسول الله صلى الله عليه وسلم يقول:إن الرقى والتمائم والتولةشرك
Daga Dan Mas'ud R.A.yace naji manzon Allah S.A.W yana cewa:Lallai Ruqya wadda bata shari'a ba,da daura/rataya laya,guru ko kambu,da sihirinda akeyi domin mallake miji,rabashi da matarsa(bita zaizai)Dukkansu shirkane.
Qarin bayani akan wannan hadithin zaizo arubutu nagaba insha Allahu.sannan kuma zamuga illoli da hatsarin da mace ke fadawa adalilin bin 'yan tsibbu,yaya qarshenta yake kasancewa.Allah yatsare mana 'yan uwanmu mata harma da mazan daga bin wannan mummunan hanya.

0 comments:

Post a Comment