• This is Slide 1 Title

    This is slide 1 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

  • This is Slide 2 Title

    This is slide 2 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

  • This is Slide 3 Title

    This is slide 3 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

Thursday, March 21, 2019

TAIMAKAMA DAN UWANKA MUSULMI DON ALLAH,ALAMANE NA IMANI

Duk cikin aikin imani taimako da dukiya yafi wahala,amma wajen masu imani sunajin sauqin taimakawa da dukiyarsu ahanyar Allah.Wanda yana daga cikin ciyarwa/taimako acikin hanyar Allah taimakama Dan uwanka musulmi wanda kasan cewa yanada buqata ko baitambayeka ba,ballantana kuma idan har ya tambayeka akan kataimaka masa.
Shaidan kuma kullum bayason yaga mumini yana taimako domin yana daga cikin abun dayake kusantar da musulmi wajen Allah shigarda farin ciki azukatan halittun Allah musamman musulmi,idan Har za'ataimaki KARE asamu aljannar Allah ina ga wanda aikinshi kenan taimakawa Dan uwanshi musulmi akan wata buqata dayake da ita/damuwa?
 Kaduba kaga yadda magbata suke aiwatar da imani azahiri;
جاء في تاريخ بغداد؛أن فقيراجاء إلى عبد الله بن المبارك،فسأله أن يقضي عنه دينا عليه سبعمائة درهم.فناوله عبد الله كتابا إلى وكيل ماله فذهب به الفقير،فلماقرأه الوكيل قال للفقير:كم الدين الذي سألت فيه عبد الله أن يقضيه عنك؟قال:سبعمائة درهم،فكتب الوكيل إلى عبد الله أن الرجل سألك أن تقضي عنه سبعمائة درهم،وكتبت له سبعةآلاف درهم،وسوف تغنى الأموال.فكتب إليه عبد الله:إن كانت الأموال قدفنيت غإن العمرأيضاقد فنى،فأجز له ماسبق به قلمي.
Ya zo acikin tarihin Baghdad,wani faqiri (matalauci) yaje wajen Abdullahi Dan Mubarak ,ya roqeshi yataimaka ya biya masa bashin da'ake binsa Dirhami dari bakwai(Dirhami 700)sai Abdullahi Dan Mubarak yarubuta takarda yabashi yakaima maikular masa da dukiya.sai wannan faqiri yatafi dawannan wasiqa(takarda) yakaimasa, Damaikula da dukiyar yakaranta sai yatambayi Faqiri nawane  bashinda kanema yabiya maka? Sai yace Dirhami 700,sai mai kula da dukiyarnan ya sake rubutawa Abdullahi Dan Mubarak cewa shifa mutuminnan bashin  Dirhami 700 yaroqi kabiya masa,kaikuma ka rubuta Dirhami 7000,ai dukiyar tana iya qarewa idan kabashi dirhami 7000.
Sai Abdullahi yasake rubuto ma maikula dakukiyarsa idan dukiya zata qare ai rayuwama tana qarewa,Kawai kabashi abunda narubuta.
 Dirhami 1 dai-dai yake da Naira 98.60,kenan faqirinnan Naira dubu sittin da Tara da naira ishirin(N69,020)ya roqi yabiya masa ,amma yabashi Dirham Dubu bakwai akudin Nigeria N690,200,haka yabashisu saboda Allah batareda ya qasqantar dashiba.
Haka akeso duk lokacin da Dan uwanka musulmi yanemi kataimaka masa to kayi kokari kabashi taimakon da bayan yamagance damuwarsa zai samu abunda zai yi amfani dashi wajen sana'ar da zata taimaka masa da iyalinsa.Wannafa itace 'yan uwantaka amusulunci.Duk lokacin da Allah yahadaka da mutane suka nemi taimakonka sai kaqi taimakonsu kuma kana da iko,to sai Allah yatambayeka,Karka biyema shaidan cewa ai wahala kayi kasamu,shi wannan dayazo neman taimako wajenka daza'abashi zabin yayi irin wahalar dakayi da zaiyi,wahalarka dan uwa ba itace ta azurtakaba ,Wallahi Allah ne ,don akwai masu irin abunda kakeyi/kayi amma basu samu abunda kasamuba.Anan duniyane kadai kakeda damar dazaka taimaki Dan uwanka.
Amma saikaga mutum Allah yarufa masa asiri,saiya dunga gudun yan uwa da abokansa,ko zuwa wajensu saikaga bayayi saboda yana ganin su basu isa yaje yaziyarcesuba.
 Wani bawan Allah yake mani korafi wata rana cewa shi wallahi yana qoqarin zuwa wajen 'yan uwansa zumunci,wani lokacinma yaje ace wai bacci sukeyi,shikuma ko hidimar gidanshi basu zuwa idanba mutuwa akayiba,ballantana kuma suzo masa ziyara haka kawai,sai yake ce Mani shi wallahi kamar yabar zuwa.Sai nace a'a kai kacigaba da zumuncin dakakeyi,ai Allah yasan zuciyarka,nakuma ce masa al'ummace yanzu idan bakada wani abu ahunnunka ba kowa ke kulakaba ballantana yazo inda kake,haka mafi yawa ake.
Allah yasanya mana tausayi acikin zukatanmu,yasa mana ganin darajar yan uwanmu musulmai da abokanenmu acikin zukatanmu.Allah karka ba shaidan dama yasamu galaba akanmu

Friday, March 15, 2019

MANZON ALLAH (S.A.W)KADAI AKEBI IDO RUFE!!!

Wallahil Azeem!!:Allah bazai tambayekaba idan bakabi,malam waneba,ko shehi waneba sannan bazai kamaka dalaifiba idan baka shiga kungiyar Izala ko Dariqa ba.
Amma tabbas Allah zai tambayeka tareda azabtarwa maitsanani idan bakabi manzon daya'aiko makaba,Muhammad swallallahu Alaihi was all am.Sannan kuma Allah zai kaamaka dalaifi idan kaqibin Qungiyar Sahabban Manzon Allah Swallallahu alaihi was all am.
Saboda duk duniya babu wanda Allah ya'aiko maka,wanda kuma dole awajensa zaka koyi addini irin kuma kafahimceshi,kuma idan kayi aikin Allah yakar6a sai Annabin Allah kuma manzonsa Muhammad Swallallahu alaihi wasallam.
قال الله تعالى:هواالذي أرسل رسوله بالهدىودين 
لحق ليظهره على الدين كله وكفى بالله شهيدا(٢٨)
محمد الرسول الله،والذين معه أشدآء على الكفار رحماء بينهم.....(٢٩)
Allah Ta'ala yana fada acikin suratul Fathi ayata 28-29 cewa:Allwh shine wanda ya'aiko manzonsa Annabi Muhammad S.A.W dashiriya dakuma addinin gaskiya(musulunci)don yarinjayarshi akan duk wani addinin dabashiba kuma lallai Allah ya'isa yazama maisheda akan hakan.
 Muhammadu Manzon Allah ne(Allah yana shedawa duniya akan masu qaryata manzoncin annabi S.A.W ,ko sunqi ko sunso Allah ya tabbatar dakasancewarshi manzonsa,wanda yazo dasaqon addinin musulunci )wa'yanda suke taredashi(sahabbansa)basu jiyar dakafirai dadi,basu sassauta mash,amma suna jinqan junansu suna tausayin junansu(suna taimakama junansu,basuson abunda zai jefa 'yan uwansu cikin halin qaqanikayi.......
Duk duniya Manzon Allah kadaine yakamata yazama madubi awajenka ,duk bunqasar malami ana binshine idan abunda yake fada ko yake koya mana yayi dai-daida karantarwar manzon Allah S.A.W.
   Saboda shikadaine binsa yake addini sa6a masa kuma yake jawoma mutum fushin Allah,kamar yadda Allah yatabbatar manada haka,cikin suratu Noor ayata 63
فليحذر الذين يخالفون عن أمره أن نصيبهم فتنة أويصيبهم عذ اب أليم
Masu sa6a umurnin manzon Allah suji  tsoron fitina sakamakon sa6a masa,ko kuma wata azaba mai radadi.
قال الله تعالى:من يطع الرسول فقد أطاع الله و من تولى فما أرسلناك عليهم حفيظا
Duk wanda yayimaka biyayya to tabbas Allah yayimawa,.....
وقال تعالى:وما ءاتاكم الرسول فخذوه ومانهاكم عنه فانتهوا،والتقوا الله،إن الله شديد العقاب(الحشر:٧)
Duk abunda manzon Allah S.A
.W yakawo muku/ya umurceku tokuriqeshi dakyau,sannan duk abunda yahaneku akansa to kuhanu daga aikatashi,kuji tsoron Allah,lallai Allah mai tsananin uqubane akan masu sa6ama umurnin manzon Allah
Kaf duniyar nan babu Wanda akaba saqon addinin musulunci sai manzon Allah,kuma ya'isar dasaqon Allah.
Wallahi babu wani abu acikin addini da idan aka aikatashi za'asamu lada fache saida manzon Allah yayi bayaninsa.
ADDININ ALLAH YAGAMA CIKA TUNKAFIN MANZON ALLAH YABAR DUNIYA,ALLAH YATABBATAR DAHAKAN.
Kuma dole saikayi Ibada yadda manzon Allah S.A.W yayi sannan zaka samu ladar abunda kayi wajen Allah.
Muhadu arubutu nagaba;Ba malam,wane,ko shehi wane aka aiko makaba.
Allah yadatardamu dabin sunnar manzon Allah  S.A.W.


Tuesday, March 12, 2019

SUGABANCIN QASATA NIGERIA

 Kai talakan Nigeria wallahi yakamata kadawo hayyacinka,dangane da qoqarin ganin ka 6ata ma wani rai akan shuwagabannin da mafi yawa batakai sukeba.Ko addini kakeyi don ka6atama wani rai to bakada lada.Amma abun mamaki dayawa daga cikin talakawa idonmu ya rufe akan wani wanda wallahi idan za'a rasaka bazaiji ko ajikinsa ballantana yaji damuwa indai har rasaka zaisa yacimma manufarsa.
 Abun mamaki wani lokacin saikaga harda malamanmu,basu auna maganganun dasuke furtawa akan siyasa dakuma Dan siyasar Nigeria.Tayadda zakaga/zakaji malami yana fadin maganganunda mai ilimin addini kuma akan fahimtar magabata nakwarai baikamata yana yinsu.Bayan duk ta bayyana babu irin rashin gaskiyarda kiwane Dan jam'iyya bayayi hasalima mafiyawan wa'yanda ake tsarkakewa abunda yayisu shiyayi wa'yanda ake zagi.
Ni haryanzu abunda kasa yarda dashi shine duk cewa duk Dan jam'iyyar su wane duk lalacewarsa,duk rashin gaskiyarsa indai Dan jam'iyyajam'iyyar wanene/suwane mutumin banzane.Shikuwa wanda baya cikin jam'iyyar suwane koda ya fi Dan jam'iyyarsu wane nagarta.
Nidai abunda nasani wanda yake saman mulki yafi damar yin magudi sama da wanda yake bashida mulki.
Kuma indai gaskiya da adalci za'ayi mutum bazai dage ala dole saiya zarce kuma kotawane hanya.
Amma tabbas yakamata mudawo mufuskanci gaskiya,babu laifi kayautatama mutum zato kuma dunga yabonshi akan kyawawan halayensa,amma hakan bai bude kofar shiga gaban Allah da manzonsaba,wajen magana da aiki kamar yadda Allah Ta'ala yafada acikin littafinsa mai tsarki:
يأيها الذين أمنواولا تقدموابين يدي الله ورسوله واتقوا الله،إن الله سميع عليم(١).
Allah ya fada cewa:ya ku wa'yanda kukayi imani(kuka bada gasikiya da Allah),karku shiga gaban Allah damanzonsa akan wajen furta wani abu aikata wani aiki acikin addinin musulunci,kuji tsoron Allah lallai Allah mai jine akan duk abunda kuke furtawa kuma mai cikakken ilimi akan duk abunda bayinsa suke aikatawa afili da boye.
 Don haka lallai mudinga taka tsan-tsan akan tsarkake kawunanmu,Domin shi Allah shikadaine yasan abundake fili da 6oye,masanin abun dayake cikin zukatan bayinsa.Tabbas akwai nagartattu acikinmu amma abudake namu shine mukyautata masu zato,tahanyar cewa da'alama wane waliyin Allah ne,tahanyar la'akarida halayen waliyyai dayakedasu cikin irin siffofinda Allah ya fada ko manzonsa S.A.W.Amma sai kaji wani harmada rantsuwa cewa wane waliyyine.Maimakon yace Wallahi duk wanda yasiffantu da siffofin waliyyai da Allah yabayyana ko manzonsa ,Wallahi waliyyine.Allah ya fada awani bangaren ayata 32 cikin suratul Najmi
فلا تزكوا أنفسكم،هو أعلم بمن اتقى.
Allah yana cewa karku tsarkake kawunanku shi Allah shine mafi sanin maijin tsoransa.
 Kawai ayi gaskiya aba jama'a wanda suka za6a,tundadai ba wahayi akayiba akan dole sai dan jam'iyya kaza yaci za'a bada mulki,shikuma dan jam'iyyar adawa idan yaci sai ayi amfanida "inconclusive ".
 . Wai anmaida shugabanci business din dayafi tara/kawo kudi masu yawa.
INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'OUN!!!

Monday, March 11, 2019

DAGA QIN GASKIYA SAI BATA!!!!

Sau dayawa idan mu yana rufewa tayadda sai ayi rashin gaskiya amma kuma maimakon wanda yayi rashin gaskiya abashi rashin gaskiyarsa sai aqirqiro wata qa'aida dandai atabbatar darashin gaskiya.
 Kamar yadda kowa yake bibiyan zabe/sakamakon zaben Kano ansan duk abunda yake faruwa har irin mummunan laifin dawani babban jami'in gwamnati yatafka wanda inda umurni za'abi kamar yadda shugaban kasa yabayyana da yayita rayuwarsa.Amma amaimakon wannan aika aika yazama abunda zai tabbatarda kasawa ta jam'iyya mai mulki a kano sai laifin yazama matakin dazai qara basu damar shirya abunda suke shirin shiryawa.
 Shifa mai abun fada baya fada,idan kuma har jam'iyyar adawa zatayi magudi amma babu wanda zai gane laifin da akayi sai "deputy Governor" to lallai akwai lauje cikin nadi.Idan kuma har amatsayinshi na mataimakin gwamna yaga wani rashin gaskiya da'akayi sai mutambayi kawunanmu:
-Ya kamata yazo yakwashe result dindin/votes?
-Ya kamata ahukunta wanda bashi yayi laifiba dalaifin marar gaskiya?
-Magana yakamata yayima wanda alhakin abun yake awuyansu ko kuwa shi doka tace yadauki mataki dakansa?
-Sannan meyatsayar dasakamakon haka har zuwa wannan lokacin?
-meke tunanin mutane idan dan jam'iyyar adawane yayi wannan katobarar?
-Anya anason kamanta adalci kuwa?
Komadai menene ita gaskita dayace tak daga kinta kuma sai bats.baikamata ace jagorori sune ke hura/rura wutar da zata iya janyo tashin hankaliba atsakanin mutanen da ake jagoranta.
Allah Ta'ala yana fada cewa kada qiyayya tasaku kuqi yin adalci/kin fadin gaskiya/aikata gaskiyarba,Allah yace kuyi adalci shine yafi kusada tsoron Allah.
Sannan Allah yace kufadi gaskiya koda akan kankune kowa'yansu nakusa daku.Saboda haka indai don al'umma akeyi to bai kamata abunda al'ummar suka zaba ahanasuba KO kuma ayi qoqarin kwace masuba.Kuma lallai yakamata wanda akejin maganarsa yayi magana tun kafin al'amari ya runcabe,wannan shine dattako kuma shine,adalci sannan kuma shine riqon amana.Daman shi adalci shine ajiye komai inda yakamata.
Nidai kam dukda ba masanin sha'ar qasa bane amma tunanina ya bani cewa it ita inec wuqa da nama duk ahannunta take,duk wani rashin adalci daza'ayi tofa idan Inec bata bayarda hadinkaiba bazai yiwuba.Don haka cewa asake yin zabe nanda sati uku masu zuwa a Nasarawa tabbas bashine hangar dayakamta abiba,saboda kenan shi mailaifi yasamu yadda yakeso kenan,mafi sharrin shugaba shine wanda mutanen dayake jagoranta bash sonshi amma shi yacije saiya mulkesu.
Kuma babu jam'iyyar idan akaqi zabanta ansabama Allah ba,indai batareda wani daliliba.Inec Kuji tsoron Allah karku jefa al'ummar Kano cikin rudanifa.Allah yakyauta yataimaki wanda al'umma keso kuma shima idan yaci Allah yabashi ikon kyautata masu kamar yadda suka bashi daman yajagorancesu.Itadai karya fure takeyi bata 'ya'ya.
GASKIYA MAI DACI!!GASKIYA MAI DACI!!

Tuesday, March 5, 2019

RAYUWA DARASINE/CE(SAMU DARASHI DUK DAGA ALLAH NE)

Darussan rayuwa sunadayawa,wani darasin yana dasauki,cikin sauqi sai kadaukeshi,wani darasin kuma akwai wahala kuma yanada wahalar dauka.Sai dai abunda yakamata idan wani yana baka labarin darasinshi to karka qaryatashi karkuma kakusheshi,yikokari kafahimci darasinshi domin maiyiwuwa za'ayima jarabawa akan irin darasinshi.
 Duk wanda zai iya tattauna darasinshi narayuwa dakai to tabbas ya yarda dakai kuma ya amince dakai domin sau dayawa darussan rayuwa suna dauke da sirrin mutum,kuma babu wanda zai bayyana sirrinshi gawanda bayaso.
   Abubuwa dadama sukansa mutum ya tunkareka da darasinshi narayuwa/sirrinshi na rayuwa,kadan daga cikinsu akwai:
1-Soyayya,
2-Qauna,
3-Yarda,
4-Zaton alkhairi,
5-Aminci,
6-Abota,
7-'Yan uwantaka tajini/addini
8-Maqotaka,
9-Fahimtarka wajen son taimako,
10-Damuwarka/kulawarka da jama'a
Idan kuwa hakane to duk wanda yazomaka dawani al'amari akan darasinshi na rayuwa,to cikin abubuwa guda biyar(5)dole asamu daya(1):
-Ko dai yazamo Dan uwanka
-Ko yazama abokinka,
-Ko yazama maqocinka,
-Ko kuma yazama qasanka yake,
-Ko kuma dalibinka.
Duk cikin wa'yannan babu wanda baicancanci kulawarkaba,gwargwadon halinda kake dashi.sannan wajen saurarensa yanada kyau kayimasa kyakkyawan fahimta.Akwai inda'yar shawara kadan yake bukata daga wajenka amma idan kajuya masa baya sai yakasa kaiwa ga inda yakeson kaiwa.Akwai kuma wanda alfarmar dayake nema wajenka idan kayi mashi babu abunda zaka ragu dashi amma sai shaidan yayi tasiri acikin zuciyarka yahanaka sanya farin ciki acikin zuciyar bayin Allah,wanda adalilin taimakama wani wajen yayewar damuwarsa/bakin cikinsa kaima Allah zai yaye maka damuwa/bakin cikin ranar alkiyama,kamar yadda manzon Allah S.A.W yafadi haka acikin ingantaccen hadithi.To shikuma shaidan yana bakin cikin mumini yasmu farinciki ranar qiyama.
Abun farko dayakamata kasa aranka duk lokacin dawani yazo da wani darasinshi na rayuwa,KAYI QOQARI KA QADDARA ACIKIN ZUCIYARKA CEWA DA KAINE KAKE CIKIN DAMUWAR DAYAKE CIKI KUMA BAKA DA HANYAR DAKAKE HANGEN YAYEWARTA AKUSA YA ZAKAJI.
KO KUMA DA KAINE KAKE NEMAN SHAWARA AKAN IRIN DAMUWAR DAYAKE CIKINTA KUMA YAKE NEMAN SHAWARAR DAZAI SAMU MAFITA,YA ZAKAYI?
Ataqaice duk lokacin dawani yazo maka dadamuwarsa/neman shawararka akan halin dayake ciki,to kajigina damuwarshi dakanka, idan Kaine awannan halin yaya zakaji.
Sau dayawa muna da dabi'ar idan dan uwanmu yazo mana dawata buqata/damuwa sai mununa masa kamar rashin imanine /rashin hakuri,a'a ba haka al'amarin yakeba,Abi Huraira R.A ya ruwaito hadithi wanda Imam Muslim yafitar dash:
عن أبي هريرة رضي الله عنه قال:خرج رسول الله صل الله عليه وسلم ذات يوم  فإذاهو بأبى بكر و عمر-رضى الله عنهما-فقال:ما أخرجكما من بيوتكما هذه الساعة؟.قالا:الجوع يا رسول الله.قال:وأنا،والذى نفسي بيده،لأخرجنى الذى أخرجكما.قوما !فقاما معه،،فأتى رجلا من الأنصار.....الى أخ
Daga Abi Huraira R.A yace:manzon Allah S.A.W yafita wata rana,sai ga Abubakar da Umar R.A.M,sai manzon Allah yatambayesu meyafito daku daga gidajenku a irin wannan lokacin?.Sai sukace:Yunwa tafito damu ya manzon Allah.Sai yace:nima,na rantseda wanda raina ke hannunsa,abunda yafito daku shiyafito dani daga gida(yunwa).Sai manzon Allah S.A.W yace: kutashi mutafi,sai sukatashi taredashi suka nufi gidan wani ansar,mutumin madina(Abu Haitham ibn Attayyihan R.A)....
Abun lura yadda manzon Allah yunwa tafito dashi daga gida tareda sauran Abokansa kuma Khalifofinsa ,nantake manzon Allah yace sutafi gidan wannan Sahabi don susamu abunda zasuci,kuma dasukaje yayi masu liyafa,har dabba yayanka masu,sukaci sukasha suka godema Allah.Dan haka duk wanda Allah ya hadaka dashi tofa yanada wani hakki akanka kaima kanada hakki akansa.
Yi kokari kazama kamar wannan sahabi mai girma dayaciyar da fiyayyen halitta S.A.W da abokansa su biyu,wajen sharema Dan uwanka kukansa.Allah yaqara mana son juna,da son taimakon juna.Allah yagafarta mana laifukanmu.

Sunday, March 3, 2019

MUHIMMANCIN SALLAH (2)

Saboda muhimmancin sallah,Allah Ta'ala ya:
*Farlanta ta ga manzonsa S.A.W acan saman samata bakwai,acikin awaje madaukaki wanda babu wani wanda zai iya kaiwa/zuwa wajen cikin halittun Allah Ta'ala.
  *Sannan Allah ya farlanta ta ga manzon Allah S.A.W,acikin mafificin dare arayuwar manzon Allah S.A.W,shine daren mi'iraji,wanda cikinsane aka hauda Manzon S.A.W zuwa cikin sammai,tun daga sama ta daya,ta biyi,ta uku,ta hudu,ta biyar,ta shida da sama ta bakwai.wanda manzon Allah yaga abubuwan ban al'ajabi wanda shikanshi mala'ika Jubrilu A.S saidai yajira manzon Allah yawuce can qololuwar sama tabakwai.
  *Yana daga cikin abunda yake nuna muhimmancin Sallah,Allah ya farlanta ta zuwa ga manzonsa S.A.W,ba tareda wasidaba atsakanin Allah da manzonsaba,ai kaitsaye manzon Allah akaba ita,sabanin sauran ibadu Mala'ika jubrilu shiyake kawoma manzon Allah S.A.W.
  *Farkon al'amari Allah ya farlanta salloli 50 akan bayinsa acikin dareda wuni(kwana1).wanda hakan yake nuna yadda Allah yake sonta,wanda bayan manzo S.A.W ya dawo samata 6 ,sai Annabi Musa A.S yakoma arage al'ummarsa bazasu iyayintaba haka,hardai ta dawo sallah biyar(5)kamar yadda akeyinta yanzu.wanda yana cikin falalar Allah darahamarsa salloli biyar akeyi amma kuma amizani ladar salloli 50 ne,wannan tabbas yana daga ni'imar Allah akan bayinsabayinsa,kenan kowace sallar farilla guda daya amatsayin salloli goma take.
  *Haryanzu saboda muhimmancinta Allah yawajabta tsarki acikin sha'aninta,tundaga karamin hadathi da babba(rihi,bawali,bayan gida,fitar maziyyi ko maniyyi ko kuma janaba),hakanan tsarkake najasa ajiki,tufafi dawajen daza'ayi sallah.Saboda masallaci(maiyin sallah) yakasance cikin hali na kamala cikakke,ai yakasance cikin tsarki zahirinsa da badininsa.
*Yana daga abunda yake nuna muhimmancinta yadda nassoshi sukazo dayawa acikin littafin Allah da Sunnar manzonsa S.A.W akan sha'aninta.
*Mutum yana kasancewa adalilin sallah,mai tsarkin jiki dakuma tsarkin zuciya,har lokacin da mutum zaishiga sallah yatsaya agaban mahaliccinsa,yana mai tsarkin zuciya,tsarkin jiki dakuma tsarkin wajenda mutum yakeyin sallar.
Duka wa'yannan suna nuna mana muhimmacin sallah,da matsayinta awajen Allah Ta'ala.
Arubutu nagaba inshaa Allah zancigaba akan falalar sallah da fa'idar da maiyinta yake samu.
   Allah yabamu dacewa.
سبحانك اللهم ربنا وبحمدك أشهد أن لا إله إلا أنت أستغفرك وأتوب إليك

MUHIMMANCIN SALLAH

Ko shakka babu sallah tanada matsayi da muhimmanci maigirman gaske awajen musulmi,yana daga muhimmancinta:
*Sallah tana daya daga cikin rukunan musulunci,kuma tana matsayi na biyu daga shahadatain(Shaidawa babu abun bauta dagaskiya sai Allah,da shaidawa lallai annabi Muhammad manzon Allah ne)kuma itace rukuni mafi girma bayan shahada.
*Kuma sallah itace ginshiqin addinin musulmi,kamar yadda manzon Allah S.A.W yafada acikin hadithi sahihi,wanda Imam Attirmizi yafjtar dashi
قال رسول الله صل الله عليه وسلم:رأس الأمر الإسلام،وعموده الصلاة،وذروةسنامه الجهاد.
Manzon Allah S.A.W ya ce:kai na al'amari shine musulunci,kuma ginshiqinsa shine sallah,tsororuwarsa (qarshensa)jihadi.
Wannan hadithi nafiyayyen halitta S.A.W cike yakeda hikima domin kamar gidane/daki ,idan babu bango to baza'a iya rufe gidanba har azauna ciki,ko kuma gini idan aka cire ginshikinshi to saman zai fado.hakanan itama sallah idan musulmi bayayi to musuluncinsa zai fado(zai lalace)

*Sallah ita kadaice atsakanin sauran rukunan musulunci bayan shahadatain(Kalmar shahada),idan mutum yabarta yana kafirta,kuma kafirci dayake fitarda mutum daga musulunci.Matsaya biyu akan wanda yabar sallah:
   1.Mutum yabar yin sallah,saboda kasala,ko kuma tozarta sallar tahanyar yinta lokacin da'akaga dama,ko yinta batare da kushu'i,ko natsuwa ba.Amma yana mai tabbatarwa azuciyarshi cewa wajibice wallah,to wannan za'ayi masa nasiha akirashi zuwa yatsaida sallah,yadunga yinta cikin jama'a.idan ya gyara to wannan haka akeso,idan kuma yacigaba akan halin dayake na wulaqanta sallah,to anan malamai sunyi sa6ani,akwai wanda sukace ya kafirta kuma idan ana shari'ar musulunci za'a kasheshi,bakuma za'ayi masa sallahba,sunkafa dalili da fadar Allah Ta'ala:
فإن تبوا وأقاموا الصلاة وأتوا الزكوة فإخوانكم في الدين
Allah yana magana akan mushrikai,idan suka tuba daga kafircin dasukeyi,suka tsayarda sallah,suka bayarda zakka,to sunzama 'yan uwanku acikin addini..
Malamai sukace acikin wannan aya ansa sharadi 3,amma duk al'amarin gudane,sharudan sune kamar haka:
-tuba daga shirka/kafirci/laifin
-tsayarda sallah
-bayarda zakka
Dole sai duka sharudan suncika mutum zaikace Dan uwa acikin musulunci.malamai sunce idan aka Sa sharadi guda days(1) ko sama da (1) akan wani abu,to abunda yake wajibi shine aciki sharudan duka ,idan daya baicikaba to kenan mutum bai cika sharadin da'aka ajiyeba.
2.Idan mutum yabar sallah yana mai inkarin wajabcinta(baiyarda cewa sallah wajibi bace),to wannan kafircine babu shakka,saboda qinyarda da wajabcin sallah ta farilla,kafircine tahanyar qaryata Allah da manzonsa,dakuma muminai.kamar yadda Allah yafada acikin suratul Nisa'i a ya ta 115:
ومن يشاقق الرسول من بعد كاتبين له الهدى ويتبع غير سبيل المؤمنين نوله ماتولى ونصره جهنم وسآءت مصيرا
Duk wanda yasa6awa manzon Allah S.A.W bayan shiriya tazo masa(anyi masa bayani), kuma yabi hanyar da bata muminaiba,Allah yace zamu ji6inta masa abunda yaji6inta kuma musashi cikin jahannama,Allah yace mokomata munana idan takasance jahannama.
Hakanan manzon Allah S.A.W yace lallai abunda yake tsakanin mutum da shirka da karfici,barin sallah.
Insha Allah zancigaba arubutu nagaba.Allah yabamu dacewa,yagafarta mana.