• This is Slide 1 Title

    This is slide 1 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

  • This is Slide 2 Title

    This is slide 2 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

  • This is Slide 3 Title

    This is slide 3 description. Go to Edit HTML and replace these sentences with your own words.

Friday, June 28, 2019

DUK WANDA KAGA YA KAUCE HANYA BA DARIYA ZAKAYIBA

Sau dadama idan mutum yaganshi cikin masu yin abunda yakamata(masu bin dokokin Allah) sai yadauka duk wanda bashiba halakakkene.
Eh tabbas duk wanda yabijirema hanyar Allah ya halaka matuqar ya mutu akan wannan mummunar hanya.Amma kai idan kaga wani ahakaba dariya zakayi ba.
Kaima ba dabararka bane dacene daga Allah.Kuma ka himmatu afili da boye wajen son kaga yadawo hanya,ta hanyar yimasa addu'a tsakaninka da Allah agaban idonsa da bayan idonsa.
Idan kasamu dama kuma sai kajawo hankalinsa akan tsayin abunda yake aikatawa.
Domin indai yazama dabi'ar mutumne tattauna matsalar wani ta bangaren  aibatawa,ko kuma kayita bibiyar mutum saika gano laifinda yake aikatawa kawai dan aibata wannan mutum to tabbas kaima akwai yiwuwar Allah yajarabceka da wannan aikin.
Sai bincike don yanke hukunci misali ga alkali akan wani mutum,ko wani maisasanci yabinciki yadda abu yafar tsakanin mutanen da suka samu rashin jituwa Dan samun maslaha shima ba laifibane.
 Rike sirrin dan uwanka musulmi yanada matuqar mahimmanci koda yaushe mudunga kyautatama 'yan uwanmu zato.Allah yasa mudace.Ameen

Wednesday, June 26, 2019

GYARA KAYANKA

Bayaushe yana karin magana dayake cewa;
Girman kai rawanin tsiya.
To tabbas wannan abu haka yake,domin shi girman yana jawo abubuwa marasa dadi ga ma'abocinsa.Kadan daga cikin illar girman kai akwai:
-yana sa maishi yakaskantar da duk wanda bashiba
-yanasa maishi ganin girman kanshi fiyeda kowa
-yanasa kafircema ni'imar Allah
-yanasa kin karbar gaskiya ko aiki da ita
-yanasa jiji dakai
-yana haifarda gaaba
-yana haifarda hassada
-yana haifarda izgilanci ga bayin Allah akan matsayin dashi Allah ya'ajiyesu
-yanasa mutum yarasa imani
-yana jawoma maiyinsa halaka
-yana haramta maishi shiga aljannah
-yana sabbaba shiga wuta
Saboda manzon Allah S.A.W yayi bayanin abunda ake cema girman kai cikin kalmomi guda biyu:
1-Raina mutane da
2-Qin gaskiya
Duka matsayin daka samu kanka karka sake ka raina mutum,sau dayawa zakaga mutum cikin 'yan uwansa ko cikin abokai idan Allah ya daukakashi saikaga duk wanda baida matsayi irin nasa bai ishesa kalloba.saiya dunga ganin kaskancine yaje yaziyarci yar uwarshi/dan uwanshi want,cibayane yakaima abokinashi want saboda wani abuda Allah yahore masa.
Bayan mazon Allah S.A.W yace:ya ishi zama laifi agaban Allah mutum yajema Allah ya qasqantarda dan uwansa musulmi.
Allah yatsaremu da girman kai,domin shine yake hana mutum karbar gaskiya saboda yana ganin Kamar duk wanda zai fada masa gaskiya baikai matsayin dazai fada mashiba.